HausaTv:
2025-07-01@17:47:42 GMT

Adadin shahidai a yakin Gaza ya kai 53,119 tun daga Oktoba 2023

Published: 17th, May 2025 GMT

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda suka yi shahada a yakin da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza ya kai 53,119 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Adadin ya karu ne sakamakon wasu hare-haren Isra’ila na baya baya nan wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 93 wayewar safiyar Juma’a.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ma’aikatar ta ce an kuma mika wasu mutane fiye da 200 da suka jikkata zuwa asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya a zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da sojojin Isra’ila suka kai a yankuna da dama.

A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an sami rahoton mutuwar mutane 109 da jikkata 216, a cewar hukumomin lafiya.

Tun bayan da Isra’ila ta sake koma kai hare-haren a ranar 18 ga Maris, adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa shahidai 2,985 da kuma jikkata 8,137.

A dunkule, tun fara harin Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin wadanda suka mutu a yanzu ya kai 53,119 da 120,214 da suka jikkata.

Kafofin yada labaran Falasdinu sun rawaito cewa sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa sama da 250 a fadin zirin Gaza musamman a yankin Beit Lahia da ke arewacin zirin Gaza cikin sa’o’i 36 kacal.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin

Sojojin HKI sun kai falasdinawa akalla 72 ga shahada a safiyar yau Litinin, daga cikinsu har da yara kanana da kuma wadanda suke jiraran a basu taimakon abinci a cibiyoyinsu a cikin Gazzar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a yau litinin a Gaza sojojin HKI sun kashe Falasdinawa a wurare da dama a gaza. Labarin ya kara da cewa an garzaya da wadanda suka ji ciwo zuwa asbitin Al-Ahli. Bayan haka yahudawan kai kai hare-hare a yankin Zaitun da kuma kasuwar zawiyya.

Labarin ya kara da cewa baba gadaje a Asbitin don haka zaka ga wadanda suka ji ciwon kwance a kasa. Har’ila yau labaran sun bayyana cewa mafi yawan wadanda sojojin yahudawa suka kashe sun kashesu ne a cibiyar bada agajin gaggawa wanda Amurka da HKI suka tsara don kashe mafi yawan adadi da zasu iya kashewa a Gaza, bayan sun hanasu abinci na kimani watanni 3.

A karshen watan mayun de ya gabata ne Amurka tare da yahudawan suka bullo da wannan tarkon don kara kashe Falasdinawa bayan sun hana shigo da abinci yankin.  Suna kashesu ne a dai-dai lokacinda suke cikin tsananin yunwa. Inda ya zama masu dole su je su nemi abinci duk inda yake.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  • Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Suna Shakku Kan Tsagaita Bude Wuta Zai Dore Da Isra’ila
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan