HausaTv:
2025-08-16@01:39:58 GMT

Adadin shahidai a yakin Gaza ya kai 53,119 tun daga Oktoba 2023

Published: 17th, May 2025 GMT

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda suka yi shahada a yakin da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza ya kai 53,119 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Adadin ya karu ne sakamakon wasu hare-haren Isra’ila na baya baya nan wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 93 wayewar safiyar Juma’a.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ma’aikatar ta ce an kuma mika wasu mutane fiye da 200 da suka jikkata zuwa asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya a zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da sojojin Isra’ila suka kai a yankuna da dama.

A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an sami rahoton mutuwar mutane 109 da jikkata 216, a cewar hukumomin lafiya.

Tun bayan da Isra’ila ta sake koma kai hare-haren a ranar 18 ga Maris, adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa shahidai 2,985 da kuma jikkata 8,137.

A dunkule, tun fara harin Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin wadanda suka mutu a yanzu ya kai 53,119 da 120,214 da suka jikkata.

Kafofin yada labaran Falasdinu sun rawaito cewa sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa sama da 250 a fadin zirin Gaza musamman a yankin Beit Lahia da ke arewacin zirin Gaza cikin sa’o’i 36 kacal.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza

Kungiyoyin kasa da kasa guda 100 sun koka kan yadda gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi watsi da bukatu har 60 kan ba da damar shigar da agaji zuwa Gaza

Sama da kungiyoyi masu zaman kansu 100 ne suka bayyana a wata wasika ta hadin gwiwa da aka buga jiya alhamis cewa, ana kara amfani da sabbin dokokin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta tsara kan ayyukan kungiyoyin agaji na kasashen waje wajen kin amincewa da bukatarsu ta shigar da kayayyaki zuwa zirin Gaza.

Wasikar ta ce: “Hukumomin gwamnatin mamayar Isra’ila sun yi watsi da bukatar da kungiyoyi masu zaman kansu da dama suka gabatar na kawo kayayyakin ceton rai, lamarin da ya bar miliyoyin daloli na agajin jin kai da suka hada da abinci, da magunguna, da ruwa, da na’urorin gaggawa, a rumbun adana kayayyaki a kasashen Jordan, Masar, da Ashdod.”

A cewar wasikar, wacce kungiyoyi irin su Oxfam da kungiyar likitocin da ba su da iyaka suka sanya wa hannu, sun fayyace cewa, an yi watsi da bukatu akalla 60 na kawo agaji cikin Gaza a watan Yuli kadai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Laifukan Cin Zarafi Musamman Kisha Kiyashi A Kasar Siyasa Ya Doshi Laifukan Yaki August 15, 2025 Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan August 15, 2025 Miliyoyin Mutane Sun Taru A Karbala Don Juyayin 40 Na Shahadarsa Imam Hussain(a) August 14, 2025 Sayyid Huthi Ya Yi gargadi Yiyuwar Tarwatsewar kasashen yankin idan HKI Ta  Tabbaga Shirinta August 14, 2025 An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London August 14, 2025 Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar August 14, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’ August 14, 2025 Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’ August 14, 2025 Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara August 14, 2025 Hizbullahi Ta Yaba Wa Iran Kan Irin Gudumawarta Ga Lebanon Da Gwagwarmaya August 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza
  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 129
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida