Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
Published: 16th, May 2025 GMT
A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267.
A cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda ya ce bikin ya nuna “wani lokaci mai muhimmanci ga mabiyan Cocin Katolika da kuma duniya da ke fama da tashe-tashen hankula da rikice-rikice da dama”.
Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ”ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami’ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980”.
A cewar sanarwar, tawagar ta shugaba Tinubu za ta haɗa da Minista a harkokin waje, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu; Archbishop Lucius Ugorji na Owerri da kuma shugaban rukunin Bishop na Katolika na Najeriya; Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja; da Alfred Martins na Legas; da kuma Bishop ɗin Katolika na Diocese na Sokoto, Mathew Hassan Kukah.
Fafaroma Leo XIV, tsohon Cardinal Robert Francis Prevost, za a rantsar da shi a matsayin Fafaroma a ranar Lahadi, 18 ga Mayu, a dandalin St Peter’s da ke Vatican.
Fafaroma Leo, wanda shi ne Fafaroma na farko daga Amurka an zaɓe shi ne kwanaki 17 bayan mutuwar magabacinsa, Fafaroma Francis, a ranar 21 ga Afrilu. Shi ne zai jagoranci Katolika biliyan 1.4 na duniya.
Ana sa ran shugaba Tinubu zai koma Abuja ranar Talata, 20 ga watan Mayu, in ji sanarwar
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Tinubu Cardinal Robert Francis Prevost Fafaroma Leo XIV sabon Fafaroma Fafaroma Leo
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar wasu sojoji huɗu, bayan ’yan ta’adda sun kai hari yankin Ngamdu na Jihar Borno.
Jihar Borno ta daɗe tana fama da hare-haren ta’addanci, musamman daga ƙungiyar Boko Haram.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno An yi jana’izar sojojin da ’yan bindiga suka kashe a KebbiKo da yake wasu mazauna yankin sun ce sojoji 10 ne suka mutu, sai dai mai magana da yawun rundunar Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, bai tabbatar da hakan ba cikin sanarwar ya fitar a ranar Juma’a.
Amma rahotanni sun bayyana cewa sojoji huɗu ne suka mutu, yayin da wasu biyar suka jikkata a yayin harin.
A cewar Kanar Sani, ’yan ta’addan sun yi amfani da roka, jirage marasa matuƙa, da bama-bamai wajen kai harin.
Sai dai sojojin sun mayar da martani, inda suka kashe da dama daga cikin ’yan ta’addan.
Ya ƙara da cewa wasu motocin yaƙi na sojojin sun lalace, amma duk da haka dakarun sun yi tsayin daka wajen yaƙar maharan.
Bayan harin, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin hana bin hanyar Ngamdu zuwa Damaturu, wanda hakan ya tilasta rufe hanyar na ɗan lokaci.
Daga baya,sojoji sun cire bama-bamai guda uku, sannan suka sake buɗe hanyar ga matafiya.
Laftanar Kanar Uba, ya ce an ƙara wa dakarun kayan yaƙi da harsasai domin ci gaba da fafatawa.
Rahotanni sun nuna cewa gawarwakin ’yan ta’adda kusan 15 aka samu a kusa da ƙauyen Bula Wura.
Rundunar Sojin Najeriya ta yaba wa jarumtar dakarun, tare da tabbatar wa jama’a cewa zaman lafiya ya samu a yankin.