Aminiya:
2025-07-01@03:30:58 GMT

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo

Published: 16th, May 2025 GMT

A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya  Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267.

Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno

A cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda ya ce bikin ya nuna “wani lokaci mai muhimmanci ga mabiyan Cocin Katolika da kuma duniya da ke fama da tashe-tashen hankula da rikice-rikice da dama”.

Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ”ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami’ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980”.

A cewar sanarwar, tawagar ta shugaba Tinubu za ta haɗa da Minista a harkokin waje, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu; Archbishop Lucius Ugorji na Owerri da kuma shugaban rukunin Bishop na Katolika na Najeriya; Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja; da Alfred Martins na Legas; da kuma Bishop ɗin Katolika na Diocese na Sokoto, Mathew Hassan Kukah.

Fafaroma Leo XIV, tsohon Cardinal Robert Francis Prevost, za a rantsar da shi a matsayin Fafaroma a ranar Lahadi, 18 ga Mayu, a dandalin St Peter’s da ke Vatican.

Fafaroma Leo, wanda shi ne Fafaroma na farko daga Amurka an zaɓe shi ne kwanaki 17 bayan mutuwar magabacinsa, Fafaroma Francis, a ranar 21 ga Afrilu. Shi ne zai jagoranci Katolika biliyan 1.4 na duniya.

Ana sa ran shugaba Tinubu zai koma Abuja ranar Talata, 20 ga watan Mayu, in ji sanarwar

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Tinubu Cardinal Robert Francis Prevost Fafaroma Leo XIV sabon Fafaroma Fafaroma Leo

এছাড়াও পড়ুন:

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe ta ƙaddamar da farautar wani mutum mai shekara 55, wanda ake zargin ya kashe matarsa ​​da adda a garin Babbangida da ke Karamar Hukumar Tarmuwa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Dungus Abdulkarim, a cikin wata sanarwa ya ce wanda wanda ake zargin ya yi wannan aika-aika ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Juma’a, 28 ga watan Yuni a kauyen Koriyel.

“Ya aikata hakan ga matarsa ’yar shekaru 40 ta hayar amfani da adda, inda ya kashe ta ya kuma tsere saboda wasu dalilai da har yanzu ba a tantance ba,” in ji sanarwar.

Tuni dai ’yan sanda suka fara kokarin cafke wanda ake zargin do ya fuskanci shari’a.

A wani labarin kuma, ’yan sanda sun kama wasu mutane biyu da kasa zargin sun kashe wani mutum bisa zargin satar waya a garin Ngalda da ke Ƙaramar Hukumar Fika.

“An zarge su ne da laifin kashe wani bisa zargin da da satar wayar hannu da na’urar cajin waya, kima dukkansu sun amince da aikata laifin kuma suna fuskantar bincike a sashen binciken manyan laifuka na jihar,” in ji shi.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar Yobe, Emmanuel Ado, ya bukaci mazauna yankin da su nemi hanyoyin warware rigingimu cikin lumana, su guji daukar doka a hannunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Yau za a yi Jana’izar Aminu Dantata a Madina
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
  • Tarihi da tasirin rayuwar Alhaji Aminu Alhassan Dantata
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu