Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
Published: 16th, May 2025 GMT
A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267.
A cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda ya ce bikin ya nuna “wani lokaci mai muhimmanci ga mabiyan Cocin Katolika da kuma duniya da ke fama da tashe-tashen hankula da rikice-rikice da dama”.
Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ”ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami’ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980”.
A cewar sanarwar, tawagar ta shugaba Tinubu za ta haɗa da Minista a harkokin waje, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu; Archbishop Lucius Ugorji na Owerri da kuma shugaban rukunin Bishop na Katolika na Najeriya; Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja; da Alfred Martins na Legas; da kuma Bishop ɗin Katolika na Diocese na Sokoto, Mathew Hassan Kukah.
Fafaroma Leo XIV, tsohon Cardinal Robert Francis Prevost, za a rantsar da shi a matsayin Fafaroma a ranar Lahadi, 18 ga Mayu, a dandalin St Peter’s da ke Vatican.
Fafaroma Leo, wanda shi ne Fafaroma na farko daga Amurka an zaɓe shi ne kwanaki 17 bayan mutuwar magabacinsa, Fafaroma Francis, a ranar 21 ga Afrilu. Shi ne zai jagoranci Katolika biliyan 1.4 na duniya.
Ana sa ran shugaba Tinubu zai koma Abuja ranar Talata, 20 ga watan Mayu, in ji sanarwar
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Tinubu Cardinal Robert Francis Prevost Fafaroma Leo XIV sabon Fafaroma Fafaroma Leo
এছাড়াও পড়ুন:
An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi
Mai martaba Sarkin Bauchi, Alhaji (Dr) Rilwanu Suleiman Adamu, ya naɗa tsohon babban jami’in Hukumar Kwastam mai ritaya, Alhaji Bala Muhammad Gidado, a matsayin Sarkin Alkaleri, wanda zai gaji marigayi Sarkin Alkaleri, Alhaji Muhammad Abdulkadir.
Da yake jawabi yayin naɗin, Sarkin Bauchi ya jaddada cewa sabon Sarkin Alkaleri ya samu wannan muƙami ne bisa la’akari da cancanta, ilimi, gogewa da kuma nagarta.
Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe Sojoji sun kashe babban Kwamandan ISWAP, Amirul Fiya a BornoYa buƙaci sabon sarkin da ya yi amfani da wannan gogewa wajen ci gaban masarauta, tare da tabbatar da gaskiya, adalci, riƙon amana da haɗin kan jama’a.
Sarkin ya yi addu’ar Allah Ya ƙara zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Bauchi, tare da yaba wa Gwamna Bala Abdulqadir Muhammad, bisa ayyukan raya ƙasa da inganta tsaro.
A nasa jawabin, shugaban ƙaramar hukumar Alkaleri, Garba Hassan Bajama, ya gode wa Sarkin Bauchi bisa tabbatar da wannan sarauta, yana mai alƙawarta haɗin kai tsakanin gwamnati da masu sarauta wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Bikin naɗin ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ‘yan siyasa, masu riƙe da muƙaman gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki, lamarin da ya nuna muhimmancin mukamin Sarkin Alkaleri a tsarin masarautar Bauchi.
Bayan naɗin, an sanya wa sabon sarki rawani da alkyabba a fadar Sarkin Bauchi, sannan jama’a suka raka shi cikin waƙe-waƙe da kaɗe-kaɗe na farin ciki zuwa garin Alkaleri.
Sabon Sarkin ya isa fadarsa a kan doki, inda aka gudanar da hawan durbar na murnar karɓar sarautar, tare da miƙa masa wuƙa, takobi da Alƙur’ani a matsayin alamar mulki.
Alhaji Bala Muhammad Gidado, wanda ya yi ritaya daga Hukumar Kwastam, yanzu shi ne Sarkin Alkaleri na tara a tarihin masarautar Bauchi.