NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
Published: 16th, May 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Jam’iyyar NNPP wadda Dakta Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu ƙarfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon Gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.
Shigowarsa ta farfaɗo da jam’iyyar, inda ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da wasu kujerun majalisa.
Sai dai rikicin cikin gida da na shugabanci sun dabaibaye jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa ficewar wasu manyan ’ya’yanta zuwa APC, lamarin da ke haifar da tambaya kan makomar NNPP a Kano.
Shin NNPP za ta kai labari a Kano, musamman bayan ficewar wasu jiga-jiganta?
NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A NajeriyaWannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dr Rabiu Musa Kwankwaso Sauya Sheƙa Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
Tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi ya ce zai yi takarar shugabancin Nijeriya a 2027 domin ba zai shiga duk wata yarjejeniyar haɗakar takara da kowa ba.
Obi wanda ya yi takarar shugabancin Nijeriya a Zaben 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar Labour (LP), ya tabbatar wa magoya bayansa cewa babu gudu babu ja da baya dangane da takararsa a babban zaɓen kasar na gaba.
An sanya dokar hana fita a Kaduna An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa TalataSai dai ya ce idan har akwai wata yarjejeniya da zai kulla, ba za ta wuce wacce za ta ba shi damar zama shugaban ƙasa na wa’adi daya ba, sannan ya miƙa wa shugaba na gaba mulki a ranar 28 ga watan Mayun 2031.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Obi ya bayyana hakan a yayin amsa tambayoyin magoya bayansa wata hira ta kai tsaye da aka yi da shi a shafin X a ranar Lahadi.
Obi ya musanta kulla yarjejeniyar tsayawa takara a karkashin tikiti daya da tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar.
Haka kuma, Obi ya ce duk wata haɗaka da za a yi wadda ba ta da kudirin kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihohin Benuwe da Zamfara…da kuma bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, to kuwa babu shi babu ita.
Kazalika, Obi ya ce yana goyon bayan tsarin da zai bayar da damar a rika karɓa-karɓar mulki a tsakanin Kudu da Arewacin Nijeriya.