Aminiya:
2025-08-16@01:38:11 GMT

Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro

Published: 16th, May 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci sojojin Najeriya su ƙara jajircewa wajen yaƙar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar nan.

Ya ce zaman lafiya, dimokuraɗiyya, da ci gaban tattalin arziƙi duk suna dogara ne da tsaron ƙasa.

An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe

Tinubu, ya bayyana hakan ne yayin wani bikin ƙaddamar da sabbin jiragen sama guda biyu ƙirar Agusta 109 Trekker a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Bikin ya kasance wani ɓangare na bukukuwan cika shekaru 61 da kafuwar Rundunar Sojin Saman Najeriya.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ne, ya wakilci Tinubu a wajen bikin.

Ya ce Najeriya na buƙatar ingantaccen tsaro domin ’yan ƙasa su samu damar yin harkokin rayuwa cikin kwanciyar hankali.

“Dimokuraɗiyya da tattalin arziƙin Najeriya na buƙatar cikakken tsaro. Dole ne a murƙushe waɗanda ke barazana ga zaman lafiya.

’Sojoji masu ƙarfi da kayan aiki masu inganci na da muhimmanci ga makomar ƙasar nan,” in ji Tinubu.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sabunta kayan aikin soji tare da saka hannun jari a fannin tsaro don tunkarar barazanar ‘yan ta’adda da sauran matsalolin tsaro.

“Wannan ci gaban zai taimaka wajen jawo saka hannun jarin a cikin gida da waje, sannan ya samar da cikakken tsaro a ƙasa,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci rundunar soji da ta kasance a shirye don samar da zaman lafiya.

A nasa jawabin, Shugaban Rundunar Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ya bayyana cewa sabbin jiragen suna da amfani matuƙa ga harkokin soji da na jin-ƙai.

Ya ƙara da cewa, tuni aka karɓi sabbin jirage tara tun daga shekarar 2024, kuma ana sa ran samun wasu 49 cikin shekaru biyu masu zuwa, ciki har da jiragen yaƙi na zamani da na ɗaukar kaya.

Abubakar, ya bayyana cewa an riga an horar da matuƙa jirage takwas da injiniyoyi 18 don aiki da sabbin jiragen, yayin da wasu ke ci gaba da karatu a ƙasashen waje.

Tinubu, ya buƙaci rundunar sojin sama da ta kula da sabbin jiragen da ƙwarewa domin amfanin ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matsalar tsaro Sabbin Jirage Tsaro yaƙi sabbin jiragen

এছাড়াও পড়ুন:

Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons

Kyaftin ɗin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta mata ta Najeriya, Super Falcons, Rasheedat Ajibade, ta ce har yanzu ba a ba su dala 100,000 da Gwamnatin Tarayya ta yi musu alƙawari bayan sun lashe gasar WAFCON a ƙasar Maroko ba.

Ajibade, ta bayyana takaicinta game da jinkirin biyan kuɗin da aka musu alƙawari.

Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

“Ba mu karɓi kuɗin ba tukunna, amma ina fata za a biya mu. Duk alƙawuran da aka mana, yanzu dai ba mu samu komai ba.”

Ajibade ta jagoranci tawagar zuwa ga nasara, inda suka sake lashe kofin WAFCON a bana.

Bayan nasarar, Shugaba Bola Tinubu ya bai wa ’yan wasan da masu horar da su lambar yabo ta ƙasa (Officer of the Order of Niger – OON).

Haka kuma ya yi musu alƙawarin bai wa kowannensu dalar Amurka 100,000 da gida mai ɗaki uku.

Lokacin da ya karɓe su a Fadar Shugaban Ƙasa, Tinubu ya yaba da jajircewarsu, da kuma ƙoƙarinsu, inda ya ce nasararsu ta ɗaga mutuncin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya
  • Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons
  • Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja