Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci sojojin Najeriya su ƙara jajircewa wajen yaƙar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar nan.
Ya ce zaman lafiya, dimokuraɗiyya, da ci gaban tattalin arziƙi duk suna dogara ne da tsaron ƙasa.
An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a YobeTinubu, ya bayyana hakan ne yayin wani bikin ƙaddamar da sabbin jiragen sama guda biyu ƙirar Agusta 109 Trekker a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Bikin ya kasance wani ɓangare na bukukuwan cika shekaru 61 da kafuwar Rundunar Sojin Saman Najeriya.
Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ne, ya wakilci Tinubu a wajen bikin.
Ya ce Najeriya na buƙatar ingantaccen tsaro domin ’yan ƙasa su samu damar yin harkokin rayuwa cikin kwanciyar hankali.
“Dimokuraɗiyya da tattalin arziƙin Najeriya na buƙatar cikakken tsaro. Dole ne a murƙushe waɗanda ke barazana ga zaman lafiya.
’Sojoji masu ƙarfi da kayan aiki masu inganci na da muhimmanci ga makomar ƙasar nan,” in ji Tinubu.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sabunta kayan aikin soji tare da saka hannun jari a fannin tsaro don tunkarar barazanar ‘yan ta’adda da sauran matsalolin tsaro.
“Wannan ci gaban zai taimaka wajen jawo saka hannun jarin a cikin gida da waje, sannan ya samar da cikakken tsaro a ƙasa,” in ji shi.
Ya kuma buƙaci rundunar soji da ta kasance a shirye don samar da zaman lafiya.
A nasa jawabin, Shugaban Rundunar Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ya bayyana cewa sabbin jiragen suna da amfani matuƙa ga harkokin soji da na jin-ƙai.
Ya ƙara da cewa, tuni aka karɓi sabbin jirage tara tun daga shekarar 2024, kuma ana sa ran samun wasu 49 cikin shekaru biyu masu zuwa, ciki har da jiragen yaƙi na zamani da na ɗaukar kaya.
Abubakar, ya bayyana cewa an riga an horar da matuƙa jirage takwas da injiniyoyi 18 don aiki da sabbin jiragen, yayin da wasu ke ci gaba da karatu a ƙasashen waje.
Tinubu, ya buƙaci rundunar sojin sama da ta kula da sabbin jiragen da ƙwarewa domin amfanin ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: matsalar tsaro Sabbin Jirage Tsaro yaƙi sabbin jiragen
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna
A cikin nuna jajircewa da hadin kai tsakanin gwamnati jiha da ta tarayya, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a ranar Juma’a ya gana da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, CON, domin yin cikakken bitar aikin titin Abuja–Kaduna–Abuja
Taron, wanda aka gudanar a birnin Abuja, ya nuna irin salon jagorancin Gwamna Uba Sani na jajircewarsa wajen tabbatar da kammala wannan muhimmin titi wanda ke da matuƙar tasiri ga tattalin arzikin ƙasa.
Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a hanzarta kammala ɓangaren Abuja–Jere da Kaduna, wanda ke da muhimmanci ga miliyoyin ‘yan Nijeriya da ke amfani da shi kullum wajen sufuri, kasuwanci da hulɗar zamantakewa.
Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.
Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.
Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”
A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.
Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.
Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.
PR: Shettima Abdullahi