Aminiya:
2025-05-16@21:24:36 GMT

Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro

Published: 16th, May 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci sojojin Najeriya su ƙara jajircewa wajen yaƙar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar nan.

Ya ce zaman lafiya, dimokuraɗiyya, da ci gaban tattalin arziƙi duk suna dogara ne da tsaron ƙasa.

An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe

Tinubu, ya bayyana hakan ne yayin wani bikin ƙaddamar da sabbin jiragen sama guda biyu ƙirar Agusta 109 Trekker a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Bikin ya kasance wani ɓangare na bukukuwan cika shekaru 61 da kafuwar Rundunar Sojin Saman Najeriya.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ne, ya wakilci Tinubu a wajen bikin.

Ya ce Najeriya na buƙatar ingantaccen tsaro domin ’yan ƙasa su samu damar yin harkokin rayuwa cikin kwanciyar hankali.

“Dimokuraɗiyya da tattalin arziƙin Najeriya na buƙatar cikakken tsaro. Dole ne a murƙushe waɗanda ke barazana ga zaman lafiya.

’Sojoji masu ƙarfi da kayan aiki masu inganci na da muhimmanci ga makomar ƙasar nan,” in ji Tinubu.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sabunta kayan aikin soji tare da saka hannun jari a fannin tsaro don tunkarar barazanar ‘yan ta’adda da sauran matsalolin tsaro.

“Wannan ci gaban zai taimaka wajen jawo saka hannun jarin a cikin gida da waje, sannan ya samar da cikakken tsaro a ƙasa,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci rundunar soji da ta kasance a shirye don samar da zaman lafiya.

A nasa jawabin, Shugaban Rundunar Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ya bayyana cewa sabbin jiragen suna da amfani matuƙa ga harkokin soji da na jin-ƙai.

Ya ƙara da cewa, tuni aka karɓi sabbin jirage tara tun daga shekarar 2024, kuma ana sa ran samun wasu 49 cikin shekaru biyu masu zuwa, ciki har da jiragen yaƙi na zamani da na ɗaukar kaya.

Abubakar, ya bayyana cewa an riga an horar da matuƙa jirage takwas da injiniyoyi 18 don aiki da sabbin jiragen, yayin da wasu ke ci gaba da karatu a ƙasashen waje.

Tinubu, ya buƙaci rundunar sojin sama da ta kula da sabbin jiragen da ƙwarewa domin amfanin ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matsalar tsaro Sabbin Jirage Tsaro yaƙi sabbin jiragen

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Shirin zai kuma samar da dubban guraben aikin yi ga matasa, wanda hakan zai rage rashin aikin yi a ƙasar.

Mutanen karkara da manoma da suka fi fama da matsalolin tsaro za su fi amfana da wannan mataki.

Shugaba Tinubu ya jaddada cewa ba za a bar masu aikata laifuka suke cin karensu ba babbaka ba.

Ya ce gwamnati za ta wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko ina a cikin Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
  • Mashawarci tsohon shugaban Ƙasa kan Sufuri Jiragen Sama ya rasu
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Karfin Tsaro Da Makamansu Masu Linzami Ne Suka Hana Makiya Kai Musu Hari
  • Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda
  • Najeriya ba za ta koma mulkin soja ba — Gowon
  • Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
  • Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi