Mashawarci tsohon shugaban Ƙasa kan Sufuri Jiragen Sama ya rasu
Published: 16th, May 2025 GMT
Kyaftin Shehu Iyali, tsohon mataimaki na musamman kan sufurin jiragen sama a zamanin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan, ya rasu.
Kyaftin Shehu Iyal ya rasu ne a ranar Alhamis bayan ya yi fama da jinya.
Kafin rasuwarsa shi ne shugaban kamfani jiragen sama mai suna Afri Air.
Marigayin yakasance jigo a harkar sufurin jiragen sama a Najeriya kuma ya tuka shugabannin ƙasa.
A shekarar 1977 Kyafin Shehu Iyal ya kammala karatun digiri ɗinsa a Jami’ar Ahmadu Bello kafin daga bisani ya shiga Kwalejin Koyon Tuƙin Jiragen Sama (NCAT) da ke Zariya.
Kafin rasuwarsa ya riƙe muƙamai da dama a fannin sufurin jiragen sama har da Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa a matsayin mai kula da sashin zirga-zirgar jirage na hukumar.
Bayanai daga iyalan marigayin na nuni da cewa za ayi jana’izar Kyaftin Shehu Iyal a yau Juma’a da yamma a unguwar Ƙwarbai cikin birnin Zariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jiragen sama Shehu Iyali jiragen sama
এছাড়াও পড়ুন:
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Ya ce, aikin wannan cibiya ta “Saudi Noor” yana gudana ne a karkashin jagorancin Hadimin wurare biyu masu tsarki; Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud, da Yarima Mohammed bin Salman.
Hakan ya nuna manufar Saudiyya wajen gudanar da ayyukan jinkai a fadin duniya—wanda KSrelief ke tallafawa al’umma—domin inganta kiwon lafiya tare da magance cututtukan dake addabar al’umma masu karamin karfi.
Ya ce, “tun lokacin da cibiyar ta fara ayyukan jinkai don yaki da cutar makanta a Nijeriya, cikin watan Oktobar 2019, KSrelief ta gudanar da gwaje-gwajen idanu sama da 218,000, da gudanar da tiyatar idanu sama da 21,000, kuma da bayar da tallafin tabarau sama da 45,000 ga al’umma.
“KSrelief ta samu karbuwa a matsayin daya daga cikin cibiyoyin jinkai a fadin duniya. Sannan kuma tun bayan kafuwar cibiyar a 2015, ta aiwatar da ayyukan jinkai sama da 3,400 a cikin kasashe sama da 107.
“Wanda a halin yanzu, ta na gudanar da ayyukan jinkan kiwon lafiya a kasashe sama da 30, musamman wajen yaki da makanta a Sudan, Yemen, Bangladesh, Mauritania, Nijeriya da sauransu.”
Ya kara da cewa, wadannan ayyukan jinkai su na tafiya kafada da kafada da manufofin kiwon lafiya na duniya tare da na Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), a fafutikar samar da lafiyar idanu ga kowa a duniya.
Wasu da dama wadanda suka ci gajiyar tallafin a Asibitin Kwararru na Potiskum sun bayyana cewa, “Wannan babban taimako ne mai muhimmanci a rayuwarmu, muna godiya ga Masarautar Saudiyya dangane da wannan tallafin.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp