Mun bijoro da wannan batun kalubalen da manoman ke ci gaba da fuskanta ne, musamman duba da cewa, kakar noman bana, ta karato, musamman ganin cewa, an fara samun saukar Ruwan sama, a wasu sassan kasar nan, inda kuma tuni, mahara suka mamaye wasu yankunan kasar da ake yin noma.

Akasarin fadin kasar nan, musamman a yankunan Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma duba da cewa, wadannan yankunan biyu, sun yi fice wajen yin noma, amma abin takaici, ‘yan bindiga daji, ‘yan ta’adda da kuma wasu Fulani Makiyaya, sun mayar da wadannan yankunan fagen daga, inda suka kashe manoma da kuma lalata amfanin gonakansu.

Bugu da kari, wadannan bata garin sun kuma kone wasu gidajen alumomin da ke a wadannan yankunan, wanda hakan ya janyo tarwatsa su, daga matsugunna su, inda kuma suka kwace yankunan.

Hakazalika, a wasu guraren, wadannan bata garin, har ma haraji da biyan wasu kudade suke  kakabawa manoma kafin su bar su, noma gonakansu ko kuma su girbe amfanin gonakansu.

Wannan matsalar ta sanya yin noma, ya fita daga ran wasu manoma da dama, wanda illar hakan, ke janyo yunwa, talauci, rashin abinci mai gina jiki a kasar.

Misali, wani rahoton hadadin guiwa a tsakanin Gwamnatin Tarayayya da Gwamnatocin jihohi tare da goyon bayan Hukumar Samar da Abinci  FAO da kuma sauran wasu masu hadaka, da aka fitar a kwanan baya ya nuna cewa, ana hasashen ‘yan Nijeriya miliyan 30.6, musamman a jihohi  26, ciki har da Abuja, ciki har da wadanda ke zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira su 150,978 za su fuskanci matsalar karancin abinci daga watannin Yuni zuwa na Agustan 2025.

Kazalika, wannan rahoton ya kula da cewa, duk da samun raguwar kayan abinci da kuma raguwar farashinsa a daukacin fadin Nijeriya, an kiyasata cewa, ‘yan kasar miliyan 24.9 cikinsu har da wadanda ke zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira a jihohi 26 ciki har da Abuja su 116,765, a yanzu haka, suna ci gaba da fuskantar karancin abinci, wanda hakan zai kara munana a cikin watan Mayun 2025.

Wata karin matsalar ita ce, hasashen kwanan baya da Bankin Duniya ya yi, na samun karuwar yunwa da fatara a 2027.

Wannan hasashen na Banki, na da nasaba da yadda Gwamnati ta yi watsi da bai wa fannin noma daukin da ya kamata, musamman, ga manona.

A saboda wadannan matsalolin da muka zayyano ne, mu a matsayin mu a wannan Jaridar, muke kalubalantar mahukuntan kasar kan cewa, ya zama wajbi su rungimi tsare-tsaren da za su warware wa manoman kasar, matsalolin da suke ci gaba da fuskanta, musaman kalubalen rashin tsaro da samar masu da kayan aikin gona a kan lokaci.

Muna kuma kalubalantar Gwamnatin da cewar, ba wai kawai ta buge da bayar da tabbaci kawai ba, amma ta dauki matakan da suka kamata, musamman domin ta tsamo manoman kasar, daga cikin kalubalen da suke ci gaba da fuskanta, domin su samu sukunin ci gaba da yin sana’arsu, ta noma.

Kazalika, muna kira ga Gwamnatin da ta samar da matakan da suka dace, na tattabar da tsaro, musamman a yankunan da ake yin noma, ta hanyar tura jami’an tsaro, da za su rinka bai wa gonakan manoma da su kansu manoman kariya daga hare-haren ‘yan bindiga daje ta kuma kafa shirye-shiyen yin aiki da ‘yansanda alumma tare da kuma samar da wata dama ta tattaunawa da shugabannin alumomi, domin lalubo da mafta kan dukka wata matsala da kunno kai a cikin alumma.

Ya zama wajbi Gwamnati ta rinka rabar da kayan aikin noma ga matasa a kan lokaci, kamar Takin zamani, ingantaccen Irin noma, magugunan feshi da sauransu.

A nan, muna bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi, a rungumi irin tsarin da Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da shi, nan a kafa Cibiyoyin rabar da kayan aikin noma guda 30, inda ta rabar da sama da kayan aikin noman rani na Shinkafa 54,000 kan farashin kaso 30.

Domin a dakile matsalar ‘yan kasuwa masu sayen amfanin gona kai tsaye daga gun manoma domin boyewa, muna kira ga Gwamnati da ta tura kayan aikin noma kai tsaye, zuwa kungiyoyin manoma wanda hakan zai bai wa manoman saukin samun rancen kudaden yin noma, samun horo da kuma samun dabarun yin noma na zamani

Ya kuma zama wajibi, Gwamnati ta samar da ababen more rayuwa a karkara, kamar inganta hanyoyin da ke a cikin karkara, samar da runbunan adama amfanin gona, rage asarar da manoma key i, in sun yi girbi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro kayan aikin noma da kayan aikin

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha

An yi girgizar kasa mai karfin daraja 5.7 a ma’aunin Richter a kasar Habasha a jiya Asabar.

Cibiyar dake kula da ilimin kasa ta kasar Jamus ta bayyana cewa, an yi girgizar kasar ne da zurfin kilo mita 10 a karkashin kasa.

Girgizar kasar ta Jiya dai tana cikin jerin girgizar da aka yi ne a cikin kasar ta Habasha a lokuta mabanbanta a wannan shekarar. Sai dai kuma a wannan loakcin ana tsoron cewa za a iya fuskantar aman duwatsu a cikin yankunan da girgizar kasar ta afku.

Daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu an yi girgizar kasa har sau 29 a cikin kasar ta Habasha, da karfin wasu daga cikinsu ya wuce daraja 5.

A  ranar 3 ga watan Janairu an yi girgizar kasa har sau 11 a rana daya sannan kuma dutsen Dopin ya yi aman wuta.

Yankin Fantali na kasar Habasha yana cikin wuraren su ka fi fuskantar aman duwatsu a tarihin kasar. A 1820 an yi wasu jerin girgizar kasa wanda ya aman wuta ya biyo baya.

A halin yanzu dai hukumomin dake kula da kasa, suna ci gaba da sa ido akan abubuwan da suke faruwa tare da yin gagradin ga mazauna yanki da su kasance cikin fadaka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida