Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo
Published: 16th, May 2025 GMT
A yayin da Babbar Sallah ke ƙara ƙaratowa, ’yan kasuwar dabbobi sun bayyana fargaba game da yiwuwar farashin raguna da sauran dabbobin lauya zai yi tashi gwauro a Najeriya.
Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin sojin ƙasar Jamhuriyar Nijar ta sanya takunkumin wucin gadi kan fitar da dabbobi zuwa ƙetare, gami da yawaitar sace-sacen dabbobi a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.
A farkon watan nan na Mayu ne Gwamnatin Nijar ta sanar cewa matakin na da nufin daidaita farashi dabbobin layya a cikin gida da kuma tabbatar da wadatarsu ga al’ummarta —waɗanda mafi rinjaye Musulmi ne — kafin zuwan Babbar Sallah a farkon watan Yuni.
Haramcin ya shafi fitar da shanu da tumaki da awaki da raƙuma, tare da alƙawarin tsauraran matakan aiwatar da dokar daga hukumomin tsaro.
Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina Faso Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?Ana fargabar wannan matakin zai yi mummunar illa ga ƙasashe kamar Najeriya da Kwaddibuwa, waɗanda suka dogara da shigo da dabbobi daga Nijar, musamman ma raguna da raƙuma a lokutan da buƙata ta yi yawa.
’Yan kasuwan Najeriya na neman mafita’Yan kasuwar dabbobi a manyan kasuwannin Kano da Jigawa na fargabar cewa matakin na gwamnatin Nijar zai iya kawo ƙarancin dabbobin da hauhawar farashi a Najeriya a lokacin Babbar Sallah.
Wani tsohon ɗan kasuwar dabbobi a kasuwar dabbobi ta Wudil a Jihar Kano, Malam Abdullahi Abdul, ya tabbatar da cewa Jamhuriyar Nijar muhimmiyar ƙasa da ke samar da raguna, musamman a lokacin sallar Layya.
Wannan lamari ya sa ’yan kasuwan Najeriya da dama neman hanyoyin samar da dabbobi daga ƙasashe kamar Kamaru da Chadi.
Yayin da ake ƙoƙarin cike giɓin, ’yan kasuwa na tunanin za a samu hauhawar farashi saboda bambancin canjin kuɗade ƙasar waje.
Alhaji Bello Guri, wani ɗan kasuwar dabbobi, ya buƙaci jama’a da kada su firgita, yana mai cewa sun fara shigowa da dabbobi Najeriya daga wasu ƙasashe.
Ya kuma yi nuni da cewa yadda mutane ke ƙara yawaita kiwon dabbobinsu na Layya zai iya rage dogaro a kan na kasuwa.
Kasuwar Maigatari ta shiga rashin tabbasKasuwar Dabbobi ta Duniya ta Maigatari a Jihar Jigawa, wadda muhimmiyar cibiya ce ga kasuwancin dabbobi daga Jamhuriyar Nijar da kuma cikin Najeriya, tana fuskantar koma baya.
Malam Dauda Babandi Gumel ya bayyana kasuwar a matsayin “kufai,” saboda ƙarancin dabbobi, a yayin da ’yan kasuwar Najeriya masu lasisin fataucin dabbobi daga Nijar ke fuskantar rashin aikin yi.
Wannan lamari ya haifar da damuwa game da yiwuwar samun ƙarancin dabbobi gabanin Babbar Sallah ta bana.
Tsadar ta damu masu sayeAlamomin kasuwa na yanzu sun nuna farashin dabbobi sun tashi sosai idan aka kwatanta da bara.
Ragon da aka sayar N120,000 a shekarar 2024 yanzu farashinsa ya kai tsakanin N170,000 zuwa N200,000. Farashin ɗan maƙi kuma ya ɗaga daga N600,000 zuwa N850,000 zuwa miliyan ɗaya.
Abbas Idris, wani mazaunin Kano, ya nuna damuwarsa cewa mutane kaɗan ne za su iya yin layya a bana idan farashin bai sauka daga yadda yake yanzu ba.
Mutane da yawa, kamar Alhaji Shehu Sharu kuma, sun zaɓi su haɗa kuɗi tare da abokansa su sayi dabbar layya saboda hauhawar farashin.
Malam Idris Isma’ila Zango, wani ma’aikacin gwamnati, ya nuna takaici cewa layya ta fi ƙarfinsa, yana mai cewa raguna sun yi tsada idan aka kwatanta da albashinsa.
Matasalar ta fi haka —MasanaBayan haramcin da Nijar ta sanar, ƙwararru irin su Dakta Aminu Rimi, masanin kasuwancin dabbobi, sun danganta hauhawar farashin ga wasu dalilai kamar yawaitar sace-sacen dabbobi da kuma gazawar manoma wajen amfani da dabarun kiwo na zamani.
Ya jaddada muhimmancin cikakken aiwatar da Shirin Zamanantar da Kiwo na Ƙasa (NLTP) don inganta samar da dabbobi.
Ibraheem Muazzam, manazarcin harkokin kasuwanci da ke Kano, ya bayyana takunkumin da Jamhuriyar Nijar ta sanya a matsayin mataki da aka yi da lissafi da dabarun siyasa daga gwamnatin sojin Nijar don tabbatar da muhimmancin ƙasar a fannin tattalin arzikin yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babbar Sallah kasuwa Layya Najeriya Nijar raguna Jamhuriyar Nijar kasuwar dabbobi Babbar Sallah
এছাড়াও পড়ুন:
Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
Biyo bayan sauya sheka da aka yi kwanan nan, a zauren majalisar dattawa, APC na da kujeru 68; PDP na da 30; LP na da 5; SDP na da 2; NNPP na da 1; APGA na da 1 da kuma kujeru guda biyu da babu kowa, guda daya daga Jihar Edo da daya daga Jihar Anambra.
Masana harkokin siyasa na ganin cewa bisa yadda lamura suke a halin yanzu, adadin na iya haurawa lokacin da majalisar tarayya ta dawo daga hutu, bayan sauya shekar Gwamna Umo Eno na Jihar Akwa Ibom daga PDP zuwa APC. Ana sa ran wasu daga cikin ‘yan majalisar tarayya na jihar za su iya bin sahunsa. A halin yanzu, Jihar Akwa Ibom tana da sanatan PDP guda biyu da ‘yan majalisar wakilai guda bakwai daga PDP.
Tun da aka rantsar da majalisar dattawa ta 10 a watan Yuni 2023, ‘yan majalisa da dama sun koma APC, wanda ya sa jam’yyar na ci gaba da samun gagarumar rinjaye.
Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba, mai wakiltar Sakkwato ta kudu na jam’iyyar PDP, ya koma APC a watan Maris 2024. Da farko, Sanata Ifeanyi Ubah ya canza sheka daga YPP zuwa APC a watan Oktoba 2023 kafin rasuwarsa.
A watan Fabrairu na 2025, Sanata Ned Munir Nwoko, mai wakiltar Delta ta arewa ya bar PDP ya koma APC, yana mai bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida a PDP na Delta ya sa ya sauya sheka.
Haka kuma, Sanata Ezenwa Onyewuchi, mai wakiltar Imo ta gabas, wanda aka zaba a karkashin jam’iyyar LP, ya koma APC a watan Yulin 2024, yana mai cewa batutuwan cikin gida ne suka jawo hakan.
Sanata Kawu Sumaila, mai wakiltar Kano ta kudu, wanda aka zabe a karkashin tutun jam’iyyar NNPP, ya sauya sheka zuwa APC a ranar 7 ga Mayu, 2025.
Bayan haka, sanatoci guda uku daga Kebbi da suka hada da Adamu Aliero, mai wakiltar Kebbi ta tsakiyar da Yahaya Abdullahi, mai wakiltar Kebbi ta arewa, da Garba Maidoki, mai wakiltar Kebbi ta kudu, suka sauya sheka daga PDP zuwa APC bayan taron da Shugaban kasa Bola Tinubu ya kira a fadar shugaban kasa.
Kazalika, tun lokacin da aka kaddamar da majalisar wakilai ta 10 a watan Yuni na shekarar 2023, wannan majalisa ya fuskanci lamarin sauya sheka ga wasu daga cikin ‘yan majalisa, wanda ya faru sakamakon sabani na ciki gida a jam’iyyu, matsin lamba na mazabu da kuma sabbin tsarin siyasa wanda hakan ya amfanar da APC.
Da farko, APC ta rike kujeru 175; PDP na da 118; LP na da 35; NNPP na da 19; APGA na da 5; ADC na da 2; SDP na da 2; YPP na da 1; yayin da kujeru uku babu kowa. Gaba daya dai, ‘yan adawar na rike da kujeru 182 fiye da APC. Amma yau, adadin kujerun ’yan adawar ya ragu zuwa 150.
An fara wannan salo ne a ranar 23 ga Yuli, 2024, lokacin da Hon. Idris Salman, mai wakiltar Kabba-Bunu/Ijumu a Jihar Kogi, ya canza sheka daga ADC zuwa APC, yana mai cewa akwai rikicin shugabanci da kuma matsi daga mazabarsa wanda ya sa ya koma jam’iyyar da ke mulki.
A watan Oktoba na 2024, Hon. Chris Nkwonta, mai wakiltar mazabar Ukwa ta yamma da Abiya ta yamma, ya bar PDP ya koma APC a ranar 2 ga Oktoba. Bayan haka a wannan watan, Hon. Sulaiman Abubakar, mai wakitar Gummi/Bukkuyum a Zamfara, shi ma ya fice daga PDP.
Jam’iyyar LP, wacce ta sami karfi a shekara ta 2023, ta fara fuskantar manyan tangarda a karshen shekarar.
A ranar 5 ga Disamba, 2024, ‘yan majalisar LP hudu cikin har da Hon. Chinedu Okere, mai wakiltar Owerri da kewaye da Hon. Mathew Donatus, mai wakiltar Kaura a Kaduna da Hon. Bassey Akiba, mai wakiltar Kalabar da kewaye /Odukpani a Kuros Ribas da Hon. Esosa Iyawe, mai wakiltar Oredo a Jijar Edo, sun koma APC, suna mai bayar da hujja kan rikice-rikicen cikin gida da suka kawo cikas ga kwazonsu.
Hon. Alfred Ajang, mai wakiltar Jos ta kudi / gabas a Filato, ya biyo bayansu a ranar 12 ga Disamba, yana jaddada dalilai masu kama da juna.
Sauyin ya ci gaba har zuwa 2025. A ranar 11 ga watan Fabrairu, Hon. Amos Magaji, mai wakiltar Zangon Kataf/Jaba a Jihar Kaduna) ya sauya sheka daga PDP zuwa APC, yana mai cewa akwai rigima a cikin jam’iyyarsa ta asali.
Washagarin ranar, Hon. Garba Koko, wai wakiltar Kebbi shi ma ya shiga APC daga PDP.
A ranar 18 ga Maris, Hon. Jallo Hussaini Mohammed, mai wakiltar Igabi a Jihar Kaduna, da Hon. Adamu Tanko, mai wakiltar Gurara/Suleja/Tafa a Neja, sun sauya sheka zuwa APC daga PDP, su yi ikirarin cewa rashin jin dadin shugabancin PDP da kuma bayyana kwarin gwiwa a gwamnatin Tinubu su ne makasudin sauya shekarsu.
A ranar 27 ga Maris, Farfesa Chinwe Clara Nnabuife, mai wakiltar Orumba ta arewa/kudu, a Jihar Anambra) ta fice daga YPP zuwa APGA, tana zargin an tsame ta daga ayyukan jam’iyyar.
A watan Mayu na shekara ta 2025, ya zama lokacin da aka sami manyan sauye-sauye. A ranar 6 ga Mayu, ‘yan majalisar PDP guda shida daga Jihar Delta sun canza sheka zuwa APC bayan gwamnan jihar, Sheriff Oborebwori ya jagoranci wannan sauyin. ‘Yan majalisar dai su ne, Hon. Bictor Nwokolo, mai wakiltar Ika arewa, gabas/Ika ta kudu da Hon. Julius Pondi, mai wakiltar Burutu da Hon. Thomas Ereyitomi, mai wakiltar mazabar Warri da Hon. Nicholas Mutu, mai wakiltar Bomadi/Patani) da Hon. Ukodhiko Jonathan, mai wakiltar mazabar Isoko da Hon. Ezechi Nnamdi, mai wakiltar Ndokwa/Ukwuani).
A ranar 15 ga watan Mayu, ‘yan majalisa biyu daga jam’iyyar NNPP, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun shiga APC. A wannan ranar, dan majalisan PDP mai wakiltar Oriade/Obokun daga Jihar Osun, Oluwole Oke, shi ma ya koma APC.
A ranar 22 ga Mayu, Hon. Sunday Umeha, mai wakitar Udi/Ezeagu daga Jihar Inugu, wanda aka zaba a karkashin LP, ya koma APC, yana cewa har yanzu matsalolin cikin gida na ci gaba da raba kawunan ‘ya’yan jam’iyyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp