Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku
Published: 16th, May 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ne ya murƙushe ƙungiyar Boko Haram lokacin da ta fara bayyana a shekarar 2002.
Atiku, wanda ya yi mataimakin shugaban ƙasa daga 1999 zuwa 2007, ya bayyana hakan ne a wata ganawa da masu ruwa da tsaki daga Jihar Kogi a birnin Abuja.
Ya bayyana cewa lokacin da Boko Haram ta fara tayar da hankali a Jihar Yobe, Obasanjo ya kira shi domin neman shawararsa.
Atiku, ya bayar da shawarar a kira shugabannin tsaro a ba su wa’adin daƙile lamarin, ko su sauka daga muƙamansu.
Obasanjo ya amince, ya kira su, ya ba su umarnin ɗaukar matakin gaggawa.
Atiku, ya ce cikin makonni kaɗan, dakarun tsaro suka murƙushe ƙungiyar Boko Haram a Yobe, kuma ba ta sake bayyana ba har sai da suka bar mulki.
Atiku, ya soki shugabannin da suka biyo bayan gwamnatinsu, inda ya bayyana cewa sun gaza ɗaukar matakin da ya dace kan matsalar tsaro.
“Babu ƙwarin gwiwar siyasa daga shugabanni,” in ji shi.
“Mutane na mutuwa, amma shugabanni ba su damu ba. Wannan babbar gazawa ce a hakar shugabanci.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.
Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.
Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.
DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar NejaWannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.
A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.
Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.
Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.
A watan Yuli 2025 Gwamna Umar Namadi ya gudanar da bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.
Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma samar da tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da zubar da jini.