Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku
Published: 16th, May 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ne ya murƙushe ƙungiyar Boko Haram lokacin da ta fara bayyana a shekarar 2002.
Atiku, wanda ya yi mataimakin shugaban ƙasa daga 1999 zuwa 2007, ya bayyana hakan ne a wata ganawa da masu ruwa da tsaki daga Jihar Kogi a birnin Abuja.
Ya bayyana cewa lokacin da Boko Haram ta fara tayar da hankali a Jihar Yobe, Obasanjo ya kira shi domin neman shawararsa.
Atiku, ya bayar da shawarar a kira shugabannin tsaro a ba su wa’adin daƙile lamarin, ko su sauka daga muƙamansu.
Obasanjo ya amince, ya kira su, ya ba su umarnin ɗaukar matakin gaggawa.
Atiku, ya ce cikin makonni kaɗan, dakarun tsaro suka murƙushe ƙungiyar Boko Haram a Yobe, kuma ba ta sake bayyana ba har sai da suka bar mulki.
Atiku, ya soki shugabannin da suka biyo bayan gwamnatinsu, inda ya bayyana cewa sun gaza ɗaukar matakin da ya dace kan matsalar tsaro.
“Babu ƙwarin gwiwar siyasa daga shugabanni,” in ji shi.
“Mutane na mutuwa, amma shugabanni ba su damu ba. Wannan babbar gazawa ce a hakar shugabanci.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Nuna Damuwarta Akan Tabarbarewar Harkokin Tsaro A Kasar Libya
A yau Alhamis ne dai kakakin ma’aikatar harkokin wajen jamhuyriyar musulunci ta Iran Dr. Isma’ila Baka’i, ya bayyana damuwar kasar akan halin da ake ciki a birnin Tripoli na kasar Libya wanda ya yi sanadiyyar kashe mutane masu dama, tare da yin kira da a kawo karshen zubar da jini.
Dr. Baka’i ya yi ishara da nauyin da ya rataya a wuyan dukkanin wadanda suke da hannu a fadace-fadacen da suke faruwa a cikin babban birnin kasar ta Libya, sannan ya bukace su da su taimaka wajen dawo da zaman tsaro a cikin kasar.
Haka nan kuma ya bukace su da su koma kan teburin tattaunawa mai maimakon amfani da karfi, su kuma kaucewa bai wa kasashen waje damar tsoma baki a cikin harkokin cikin gidansu.
Dr. Baka’i, ya kuma mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda rikicin na kasar ta Libya ya rutsa da su, da kuma yin addu’ar samun sauki ga wadanda suka jikkata.