Shugaban hukumar Makamashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Eslami ya bayyana cewa kasarsa bata boye wani wuri inda take sarrafa makamashin Nukliya wanda bata fadawa hukumar IAEA ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Islami yana fadar haka a jiya Laraba, kuma don kare matsayin Iran na mallakar fasahar nukliya ta zama lafiya, wanda kasashen yamma suke zarginta da kokarin kere makaman nukliya.

Shugaban hukumar makamashin Nukliya ta kasar Iran ya bayyana haka ne a gefen taro Makamashin Nukliya na kasar Iran karo na 31 wanda aka gudanar a nan birnin Tehran, ya kuma kara da cewa babu wata cibiyar sarrafa makamashin nukliya wanda Iran ta boyewa hukumar IAEA a da ko yanzu. Kuma da akwai hakan da sun gane tunda hukumar ta IAEA tana da ma’aikata da kuma kamerori wadanda zasu iay gane duk inda aka boye makamacin uranaim.

Dangane da tattaunawan da JMI take yi da Amurka kan shirinta na makamashin Nukliya kuma Eslami ya bayana cewa, har yanzun tattaunawar bat shiga tafsili dalla-dalla na shirin Nukliyar kasar ba. Amma dayan bangaren ya dogara da farfaganda da kuma takurawar kawayenta don cimma wasu manufofinta a cikin tattaunawar.

Shugaban hukumar makamashin nukliya ta kasar Iran y ace, kuma ya sake nanatawa, shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce. Babu wata manufa a boye don kera makaman nukliya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makamashin nukliya makamashin Nukliya Shugaban hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta

Hukuma mai kula da sauka da tashin jiragen sama a birnin Paris ya dakatar da wani ma’aikacinsa, wanda yake aikin a bangaren kula da sauka da tashin jiragen sama, saboda ya shelantawa wani jirin HKI wanda ke kokarin sauka a tashar jiragen kan cewa “yanci-yenci Falasdinu”.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto majiyar kafafen yana labarai na kasar Faransa na cewa, ma’aikacin ya fadi wadannan kalmomi ne ga matukin HKI wanda ya tashi a tashar ‘Charles de Gaulle’ da ke birnin Paris.

Labarin ya kara da cewa matukin jirgin ne ya bada wannan rahoton ga hukumomin kasar Faransa don daukar matakin da ya dace.

Ba’a bayyana sunan ma’aikacin ba, amma a jiya talata ce hakan ya auku, inda bayan tashin jirgin kafin ya sallami matukin jirgin yayi wadannan kalmomi na “frre palastain” wato enci ga Falasdinu.

A halin yanzu dai ministan sifiri na kasar faransa Philippe Tabarrot  ya bada sanarwan cewa an dakatar da ma’aikacin da yayi hakan, kuma za’a gudanar da bincike don ladabtar da shi nan gaba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy August 13, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe August 13, 2025 Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe August 13, 2025 Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin August 13, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida  August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Habasha: Madatsar ruwanmu amfanin dukkanin kasashen yankin ne August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fushin Sojojin Kasar
  • Larijani: Iraki Bata Daukan Umarni Daga JMI
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Gobe Talata
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre