NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa
Published: 15th, May 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta yi amai ta lashe.
Bayan ta musanta duk zarge-zargen da aka yi cewa tana da hannu a rashin kyawun sakamakon jarabawar da ta shirya, shugaban hukumar ya fito ya amsa laifin.
Yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai, Farfesa Is-haq Oloyede ya ce dalibai 379,997 abin ya shafa, kuma hukumar za ta sake shirya musu wata jarabawar.
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne a kan dalilan Hukumar ta JAMB.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
Matar da ta daina ganin girman mijinta ta riga ta fara ruguza aurenta, da zarar kin yi masa maganganu na cin mutunci, kin yi kamar kin tozarta kanki da kanki ne, saboda girman mace a cikin aurenta yana da alaka da girman mijinta.
2. Rashin adalci tsakanin mijinki da danginsa
Ki sani, mijinki zai iya jure miki a kuskuren da kike masa kai tsaye, amma zai dade yana daukar zafin abin da kika aikata wa iyayensa, ‘yan uwansa ko danginsa, wannan babban kuskure ne da mata da dama suke yi su kuma yi nadama daga baya.
3. Rashin Tausayi da Kulawa
Ki sani, koda kuwa mijinki yana da kudi, yana bukatar jin tausayi daga gare ki. Idan ya dawo gida a gajiye, kuma ba kya nuna damuwarki ko kulawarki, hakan na iya sanyawa ya ji babu darajarsa a idonki. Wannan ma yana daga cikin manyan kurakuran da ake nadama a kai.
4. Yin kishi nai tauri da rashin amana
Kishin mace al’ada ne, amma idan ya wuce kima, yana canza soyayya zuwa guba. Idan baki yarda da mijinki ba, kina tuhumarsa a kan kowanne abu, to ke da kanki za ki gaji, shi ma ya gaji, sai aure ya fara tangal-tangal.
Za Mu Ci Gaba Mako Mai Zuwa In Allah Ya Kai Mu
ShareTweetSendShare MASU ALAKA