NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa
Published: 15th, May 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta yi amai ta lashe.
Bayan ta musanta duk zarge-zargen da aka yi cewa tana da hannu a rashin kyawun sakamakon jarabawar da ta shirya, shugaban hukumar ya fito ya amsa laifin.
Yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai, Farfesa Is-haq Oloyede ya ce dalibai 379,997 abin ya shafa, kuma hukumar za ta sake shirya musu wata jarabawar.
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne a kan dalilan Hukumar ta JAMB.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
Hukumar tsaro ta sibil difens (NSCDC) ta sanar da cafke wani mutum, Salisu Muhammad, mai shekaru 45, bisa zargin kashe jami’inta, Bashir Adamu Jibrin, a kasuwar Shuwarin da ke Karamar Hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Muhammed Badarudeen ya fitar a Dutse, babban birnin jihar, lamarin ya faru ne a ranar kasuwa lokacin da marigayin yake gudanar da aikinsa.
Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani Tankokin mai sun yi bindiga a ZariyaRahotanni sun nuna cewa, ana zargin Salisu ya buga wa jami’in dutse a kai, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.
Hukumar ta ce ta kama wanda ake zargin ne a gidansa da ke Shuwarin a ranar 7 ga watan Agusta, 2025.
Sai dai bayanai sun ce Salisu wanda bai cimma nasara ba yayi ƙoƙarin tserewa a yayin da ake jigilar sa zuwa hedikwatar NSCDC da ke Dutse a cikin motar jami’an tsaron.
Sanarwar ta ƙara da cewa, Salisu ya samu raunuka ne yayin da yake ƙoƙarin tserewa, kuma daga bisani aka kai shi babban asibitin Dutse, inda aka tabbatar da rasuwarsa sakamakon raunikan da ya samu.
Sai dai ’yan uwansa sun buƙaci cikakken bayani dangane da raunikan da ya samu har da dalilin rasuwarsa a asibitin Sambo Limited wanda aka garzaya da shi bayan ya yi yunƙrin tserewa daga mota da ke tafe.