Aminiya:
2025-06-23@06:32:25 GMT

Gwamna Buni ya tallafawa iyalan sojojin da suka mutu 

Published: 9th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a ranar Alhamis ya ziyarci sojojin Hedikwatar Task Force Brigade ta 27 Buni Gari, domin jajantawa waɗanda aka kashe kan harin da ’yan tada ƙayar baya suka kai. 

A cikin jawabinsa Gwamna Buni ya bayyana cewa, abin takaici ne ga sake ɓarkewar tashe-tashen hankula da kuma hare-haren da ake kaiwa jami’an tsaro.

’Yan sanda sun ƙaddamar da ƙwararrun Jami’an tsaro saboda makarantu a Bauchi An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna

Gwamnan ya jajanta wa sojoji da iyalan ma’aikatan da suka mutu, yana mai cewa, “Jami’an ba su mutu a banza ba, sun mutu suna ƙoƙarin kare ƙasarsu sosai”.

Ya bayar da tallafin Naira miliyan 2m ga kowane iyalan jaruman da suka mutu, sannan kuma Naira miliyan 1m ga jami’an da suka samu raunuka.

Buni ya ce, gwamnati za ta kuma bayar da tallafin ilimi kyauta ga yaran sojojin da suka mutu.

Hakazalika, Gwamnan ya sanar da bayar da gudunmuwar Naira miliyan 50 da za a raba wa dakarun rundunar ta 27 Brigade Buni Gari, baya ga kayan abinci, katifa, barguna da sauran kayayyaki da gwamnatin jihar ta bayar.

Ya kuma ba da tabbacin goyon bayan gwamnati da al’ummar jihar ga sojoji da sauran jami’an tsaro domin yaƙar waɗannan ’yan ta’addan yadda ya kamata tare da fatattakarsu.

Gwamna Buni ya ba da umarnin ƙarfafa tsaro a kewayen rundunar, inda ya ba da tabbacin goyon bayan gwamnati ga jami’an tsaro, “Za mu ci gaba da ƙara ƙaimi wajen inganta tsaro a kewayen.

Kwamandan rundunar Birgediya Janar Usman Ahmed, wanda ya jagoranci Gwamnan wajen duba wannan runduna, ya yabawa Gwamna Buni kan yadda ya ke nuna damuwa da kulawa ga sojojin a kowane lokaci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buni Gari Gwamnan Jihar Yobe jami an tsaro Gwamna Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila

Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv.

Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500.

Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci.

Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran.

Makamin ya faɗo kan cibiyar ne kafin wayewar garin ranar Lahadi, amma babu wanda ya ji rauni domin cibiyar ba kowa a cikinta a lokacin.

Fira Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya ziyarci wurin, inda ya ce, “wannan harin ne dalilin da ya sa Isra’ila ba za a taɓa barin Iran ta mallaki makaman nukiliya ba.”

Idan ba a manta ba, Isra’ila ce ta fara kai hari kan Iran a ranar 13 ga Yuni, bisa hujjar cewa abokiyar gabar tata tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Iran, wadda ta dage cewa shirin nukiliyarta don dalilai na zaman lafiya ne kawai, ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami da na jirage marasa matuƙa a kan Isra’ila.

Hare-haren Isra’ila sun yi sanadiyar mutuwar wasu manyan masana kimiyyar nukiliya na Iran, da manyan shugabannin sojojin Iran, da fararen hula tare da lalata gidaje da tashoshin nukiliya da ababen more rayuwa.

Duk da cewa yawancin binciken cibiyar Weizmann sun danganci fannin gas magunguna da ilimin kimiyya ne, amma tana kuma da alaka da tsaro.

A watan Oktoba na 2024, ta sanar da haɗin gwiwa da babban kamfanin tsaro na Isra’ila, Elbit, kan “kayayyakin da aka samo daga halittu don aikace-aikacen tsaro.”

Cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, tana da ƙungiyoyin bincike 286, masana kimiyya ma’aikata 191, da daruruwan dalibai.

Iran ta sanar a ranar Juma’a cewa ba za ta tattauna makomar shirin nukiliyarta ba yayin da take fama da hare-hare daga Isra’ila.

Duk ƙoƙarin ƙasashen Turai na jan hankalin Tehran zuwa tattaunawa bai nuna alamun nasara ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila
  • Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Ambaliyar Ruwan Mokwa: Masana Sun Shawarci Gwamnati Kan Matakin Kariya A Nan Gaba
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya