Babban Sufeto Janar na ’yan sandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya ƙaddamar da Ƙwararrun Jami’an tsaro da za su kare makarantu a Bauchi, Egbetokun ya ƙaddamar da tawagar ne a ranar Alhamis a Bauchi.

A wajen ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na ‘Saɓe Schools’ a ɗakin taro na otal ɗin Hazibal.  Ya ce, ta hanyar haɗa kai da masu ruwa da tsaki ne jami’an tsaro za su iya kaiwa ga samar da ingantaccen tsaro a makarantu ga yaran Najeriya.

An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna An zaɓi Robert Prevost sabon fafaroma

Egbetokun wanda ya samu wakilcin AIG Abubakar Sadiƙ Aliyu, ya shawarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa da tunaninsa wajen samar da sabbin dabaru da tsare-tsare masu inganci waɗanda za su inganta tsaro da ƙarƙo a makarantun jihar.

Ya ce, rundunar na daga cikin tsare-tsaren kare lafiya a makarantu da Sufeto Janar na ’yan sanda, Kayode Egbetokun ya ɓullo da shi kuma ya umurci Kwamishinonin ’yan sanda na jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja da su haɗa hannu da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaron makarantu daidai da tsarin da aka yi a ƙasa baki ɗaya.

Egbetokun ya bayyana shirin a matsayin wani gagarumin ci gaba ga tsarin da ya haɗa da kare makarantu cikin aminci da sauran muhallin koyo.

Ya ce, ya zama wajibi hukumomin ilimi na Najeriya da shugabannin al’umma su haɗa kai da jami’an tsaro wajen ƙarfafawa da kuma kare makarantun daga duk wata barazana.

Ya kuma ba da tabbacin cewa, ’yan sanda a shirye suke a kodayaushe don ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi da kuma tabbatar da yanayin koyo mai kyau da aminci  ga ɗalibai.

Gwamna Bala Mohammed ya ce, ya kamata hukumomin tsaro daban-daban su faɗakar da wasu shugabannin ɗalibai da ƙungiyoyinsu dabarun gano duk wata barazana da sanar da hukumomin tsaro cikin lokaci.

Gwamna Bala wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tsaro, AIG Ahmed Abdulrahman ya shawarci shugabannin ɗaliban da su yi amfani da hanyar da ta dace wajen sanar da Jami’an tsaro a duk lokacin da suka ga wani mutum ko wani lamari da ya taso.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omoloro Aliyu ya yi ƙarin haske kan yadda ake samun ƙaruwar satar mutane, hare-hare da tashe-tashen hankula da ake kai wa makarantu, ɗalibai da ma’aikatu.

“Wadannan munanan al’amura ba wai kawai sun kawo cikas ga harkar ilimi ba, har ma sun sanya tsoro da fargaba a tsakanin iyaye, ɗalibai da kuma al’ummar ƙasa baki ɗaya, wanda ’yan sanda tare da haɗin gwiwar gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki daban-daban suka mayar da martani tare da samar da shirin kare makarantunmu cikin aminci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda ma aikatun Gwamnatin Tarayya masu ruwa da tsaki kare makarantu ƙaddamar da Egbetokun ya a makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi

’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.

’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba

A cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.

Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.

Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Gamayyar Ƙungiyoyin Tinubu/Shettima Za Su Ƙaddamar Da Gangamin Yaƙi Da Masu Yi Wa Tafiyar Shetttima Zagon Ƙasa – Aminu Boyi 
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila
  • Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya