’Yan sanda sun ƙaddamar da ƙwararrun Jami’an tsaro saboda makarantu a Bauchi
Published: 9th, May 2025 GMT
Babban Sufeto Janar na ’yan sandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya ƙaddamar da Ƙwararrun Jami’an tsaro da za su kare makarantu a Bauchi, Egbetokun ya ƙaddamar da tawagar ne a ranar Alhamis a Bauchi.
A wajen ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na ‘Saɓe Schools’ a ɗakin taro na otal ɗin Hazibal. Ya ce, ta hanyar haɗa kai da masu ruwa da tsaki ne jami’an tsaro za su iya kaiwa ga samar da ingantaccen tsaro a makarantu ga yaran Najeriya.
Egbetokun wanda ya samu wakilcin AIG Abubakar Sadiƙ Aliyu, ya shawarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa da tunaninsa wajen samar da sabbin dabaru da tsare-tsare masu inganci waɗanda za su inganta tsaro da ƙarƙo a makarantun jihar.
Ya ce, rundunar na daga cikin tsare-tsaren kare lafiya a makarantu da Sufeto Janar na ’yan sanda, Kayode Egbetokun ya ɓullo da shi kuma ya umurci Kwamishinonin ’yan sanda na jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja da su haɗa hannu da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaron makarantu daidai da tsarin da aka yi a ƙasa baki ɗaya.
Egbetokun ya bayyana shirin a matsayin wani gagarumin ci gaba ga tsarin da ya haɗa da kare makarantu cikin aminci da sauran muhallin koyo.
Ya ce, ya zama wajibi hukumomin ilimi na Najeriya da shugabannin al’umma su haɗa kai da jami’an tsaro wajen ƙarfafawa da kuma kare makarantun daga duk wata barazana.
Ya kuma ba da tabbacin cewa, ’yan sanda a shirye suke a kodayaushe don ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi da kuma tabbatar da yanayin koyo mai kyau da aminci ga ɗalibai.
Gwamna Bala Mohammed ya ce, ya kamata hukumomin tsaro daban-daban su faɗakar da wasu shugabannin ɗalibai da ƙungiyoyinsu dabarun gano duk wata barazana da sanar da hukumomin tsaro cikin lokaci.
Gwamna Bala wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tsaro, AIG Ahmed Abdulrahman ya shawarci shugabannin ɗaliban da su yi amfani da hanyar da ta dace wajen sanar da Jami’an tsaro a duk lokacin da suka ga wani mutum ko wani lamari da ya taso.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omoloro Aliyu ya yi ƙarin haske kan yadda ake samun ƙaruwar satar mutane, hare-hare da tashe-tashen hankula da ake kai wa makarantu, ɗalibai da ma’aikatu.
“Wadannan munanan al’amura ba wai kawai sun kawo cikas ga harkar ilimi ba, har ma sun sanya tsoro da fargaba a tsakanin iyaye, ɗalibai da kuma al’ummar ƙasa baki ɗaya, wanda ’yan sanda tare da haɗin gwiwar gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki daban-daban suka mayar da martani tare da samar da shirin kare makarantunmu cikin aminci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda ma aikatun Gwamnatin Tarayya masu ruwa da tsaki kare makarantu ƙaddamar da Egbetokun ya a makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai wajen magance matsalar rashin tsaro a faɗin ƙasar cikin shekaru biyu da suka gabata.
Shugaban ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na daƙile ayyukan ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiyar ƙasa.
Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masaiA wata sanarwa da Tinubu ya fitar a shafinsa na sada zumunta, a ranar Juma’a, ya ce ƙalubalen tsaro a Najeriya, da suka haɗa da ta’addanci da aikata laifuka, ana magance su da sabbin tsari da sauye-sauyen dabarun dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.
“Haƙiƙa muna fuskantar ta’addanci – ƙalubalen da Najeriya ta fuskanta kusan shekaru ashirin, kuma ba za mu ja da baya ba, za mu yi nasara a kan ta’addanci kuma mu yi iƙirarin samun nasara a wannan yaƙin, ba za mu taɓa yin sulhu harkar tsaro ba.
“Najeriya ƙasa ɗaya ce mai haɗin kai, mun tashi tare, mun ci gaba tare, kuma mun ƙi yanke ƙauna domin tabbatar da ƙuduri.
“Aikin da ke gabanmu yana da yawa, amma duk da haka ƙudurinmu ya fi girma, za mu ci gaba da ɗorewa tare da inganta nasarorin da muka samu na sake fasalin ƙasa da kuma samar da ci gaba a Najeriya.
“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba kuma ba za mu bar wani abu ba a cikin aikinmu na kawar da masu aikata laifuka a cikin al’ummarmu, muna kira ga abokan haɗin gwiwarmu da su tsaya tsayin daka tare da mu yayin da muke ƙara faɗaɗa yaƙin da muke yi da ta’addanci, mun samu gagarumin ci gaba a cikin shekaru biyu da suka gabata, kuma za mu kawar da wannan barazana.”