Babban Sufeto Janar na ’yan sandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya ƙaddamar da Ƙwararrun Jami’an tsaro da za su kare makarantu a Bauchi, Egbetokun ya ƙaddamar da tawagar ne a ranar Alhamis a Bauchi.

A wajen ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na ‘Saɓe Schools’ a ɗakin taro na otal ɗin Hazibal.  Ya ce, ta hanyar haɗa kai da masu ruwa da tsaki ne jami’an tsaro za su iya kaiwa ga samar da ingantaccen tsaro a makarantu ga yaran Najeriya.

An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna An zaɓi Robert Prevost sabon fafaroma

Egbetokun wanda ya samu wakilcin AIG Abubakar Sadiƙ Aliyu, ya shawarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa da tunaninsa wajen samar da sabbin dabaru da tsare-tsare masu inganci waɗanda za su inganta tsaro da ƙarƙo a makarantun jihar.

Ya ce, rundunar na daga cikin tsare-tsaren kare lafiya a makarantu da Sufeto Janar na ’yan sanda, Kayode Egbetokun ya ɓullo da shi kuma ya umurci Kwamishinonin ’yan sanda na jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja da su haɗa hannu da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaron makarantu daidai da tsarin da aka yi a ƙasa baki ɗaya.

Egbetokun ya bayyana shirin a matsayin wani gagarumin ci gaba ga tsarin da ya haɗa da kare makarantu cikin aminci da sauran muhallin koyo.

Ya ce, ya zama wajibi hukumomin ilimi na Najeriya da shugabannin al’umma su haɗa kai da jami’an tsaro wajen ƙarfafawa da kuma kare makarantun daga duk wata barazana.

Ya kuma ba da tabbacin cewa, ’yan sanda a shirye suke a kodayaushe don ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi da kuma tabbatar da yanayin koyo mai kyau da aminci  ga ɗalibai.

Gwamna Bala Mohammed ya ce, ya kamata hukumomin tsaro daban-daban su faɗakar da wasu shugabannin ɗalibai da ƙungiyoyinsu dabarun gano duk wata barazana da sanar da hukumomin tsaro cikin lokaci.

Gwamna Bala wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tsaro, AIG Ahmed Abdulrahman ya shawarci shugabannin ɗaliban da su yi amfani da hanyar da ta dace wajen sanar da Jami’an tsaro a duk lokacin da suka ga wani mutum ko wani lamari da ya taso.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omoloro Aliyu ya yi ƙarin haske kan yadda ake samun ƙaruwar satar mutane, hare-hare da tashe-tashen hankula da ake kai wa makarantu, ɗalibai da ma’aikatu.

“Wadannan munanan al’amura ba wai kawai sun kawo cikas ga harkar ilimi ba, har ma sun sanya tsoro da fargaba a tsakanin iyaye, ɗalibai da kuma al’ummar ƙasa baki ɗaya, wanda ’yan sanda tare da haɗin gwiwar gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki daban-daban suka mayar da martani tare da samar da shirin kare makarantunmu cikin aminci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda ma aikatun Gwamnatin Tarayya masu ruwa da tsaki kare makarantu ƙaddamar da Egbetokun ya a makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI

Ya gargadi cewa, tarihi ba zai gafarta wa shugabannin Arewa ba idan suka kasa daukar matakin gaggawa wajen dakile kashe-kashe, garkuwa da mutane da rikice-rikicen da ke addabar yankin. Ya ce shiru da fifita wasu akan wasu daga cikin shugabanni suna kara ta’azzara matsalar tsaro a jihohin Zamfara, Kaduna, Katsina, Filato da Benuwe.

 

Ya bayyana cewa akwai damuwa matuka yayin da ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, wasu daga cikin manyan mutane na fifita shirya shagulgula masu tsada maimakon kiraye-kirayen tarurrukan neman mafita na gaske don kawo karshen wannan rikici.

 

“Lokacin yin shiru ya wuce, yanzu ne lokacin daukar mataki. Tarihi ba zai gafarta wa halin ko-in-kula ba a lokacin da ake bukatar mataki fiye da kowane lokaci.”

 

Idris ya ce kungiyarsu na cikin damuwa matuka bisa abin da ya kira “ƙin ɗaukar mataki na gaggawa daga hukumomin tsaro duk da bayanan sirri da ke hannunsu, lamarin da ya bar gwamnonin jihohi cikin wahala da kuma barin ‘yan kasa cikin hali na shakku da rashin tsaro:.

 

Ya kuma bukaci ‘yan Arewa da su kaurace wa rarrabuwar kawuna, yana mai jaddada cewa tsawon ƙarnuka mutane masu bambancin addinai da kabilu sun zauna tare cikin zaman lafiya.

 

Har ila yau, dole ne a fahimci zaman lafiya ba wai kawai rashin rikici ba ne, har da nufin kasancewar adalci, da mutunci ga kowa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro
  • Ranar Zaman Lafiya ta Duniya: Kungiyar Arewa Ta Nemi Ƙarfafa Sirrin Tsaro Don Kare ‘Yan Najeriya