Aragchi: Muna Bukatar Rage Zaman Daradar Da Kuma Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Pakisatan Da Indiya
Published: 8th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa akwai bukatar kasashen Indiya da Pakisatan su daure su daina musayar wuta a tsakaninsu saboda tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a safiyar yau Alhamis bayan isarsa birnin News Delhi.
A jiya larabace sojojin kasar Indiya suka cilla makamai masu linzami kan kasar Pakisatan da kuma yankin Kashamir da ke karkashinn ikon Pakisatn. Inda mutane 31n sauka rasa rayukansu a yayinda wasu 46 suka suka ji Rauni.
Shehbaz Sharif firai ministan kasarPakisatan ya bayyana cewa kasar Pakisatan zata rama, kuma ya sha alwashin maida martani kan duk wani jinin mutanen Pakisatan da sojojin Indiya suka zubar.
Har’ila yau ministan harkokinn wajen kasar Iran ya je kasar ta Indiya ne don halattan taron kwamitin tattalin arziki na hadin giwa tsakanin kasashen biyu. Ministan ya kara da cewa zai tattauna da tokwaransa na kasar Indiya kan yakin da ya barke a tsakanin kasashen biyu.
Sannan a wani labarin kuma kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bakaei ya bayyana cewa kasashen Indiya da Iran zasu rattaba hannu a kan wasu yarjeniyoyi tsakanin kasashen biyu a wannan ziyarar Aragchi zuwa kasar ta Indiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hizbullah Ta ce Marigayi Shahid Ra’isi Ya Kasance Mai Taimakawa Kasar Lebanon Da Kuma Falasdinawa Ne
Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sayyid Na’im Kasim a wani jawabinda da ya gabatar don tunawa da cika shekara guda da shahadar shugaban kasar Iran Sayyid Ibrahim Ra’isi da abokan tafiyarsa, ya bayyana cewa shugaban ya kasance mai kaunar falasdinawa ne har cikin zuciyarsa.
Sheikh Qasim ya kara da cewa, shugaba Ra’isi ya rike makamai da dama a rayuwarsa a JMI amma wannan bai canza shi ba, ya kasance yana tambaya ta dangane da gwagwarmaya da HKI a yankin Hizbullah da kuma sauran mujahidai a yankin.
A lokacin shugabancinsa ya taimakawa kungiyar Hizbullah, sosai kamar yanda wadanda suka gabaceshi suka yi. A ranar 20 ga watan Mayun shekarar da ta gabata ce. Sayyid Ibrahim Ra’isi shugaban kasar Iran yayi hatsari da jirgin sama mai saukar ungulu a kan hanyar dawowarsa daga makobciyar kasar Azerbai jan inda da shi da ministansa na harkokin waje da kuma limamin masallacin jumma’a na birnin Tabriz duk suka rasa rayukansu a hatsarin.