Aminiya:
2025-08-07@12:54:14 GMT

A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci – Ganduje

Published: 8th, May 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da shawarar yin amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan fashi a Nijeriya.

Shugaban ya bayar da shawarar ne a ranar Larabar da ta gabata a lokacin da ya jagoranci mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na ƙasa a ziyarar jaje ga gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a kan harin da aka kai wa rundunar sojijin barikin soja da ke Buni Gari.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’

Ganduje ya ce dole ne yaƙi da ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi da makami su tafi tare da haƙiƙanin lokaci domin samun nasara.

Ya bayyana cewa abin takaici ne irin yadda ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi suke aikata munanan ayyuka a faɗin ƙasar nan.

“A yanzu za a yi amfani da albarkatun da ake da su don maye gurbin irin kayan aikin da aka lalata.”

Da yake jawabi, gwamna Buni ya ce gwamnati a matakai daban-daban na duba yadda ake amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ‘yan ta’adda.

“Mu, a matakin ƙasa da gwamnonin yankin Tafkin Chadi, muna yin nazari sosai kan yadda maƙiya ke amfani da jirage marasa matuƙa aikata ta’assar wadda dole mu haɗa kai da jami’an tsaro don duba matsalar,” in ji Buni.

Ya ba da tabbacin cewa za a tattauna hakan a mataki mafi girma musamman da shugaban ƙasa domin daƙile ayyukan tada ƙayar baya da ’yan bindiga.

“Wannan matsala ce ta ƙasa domin a lokacin da suka kai hari a sansanin soji da kuma ƙwace makamai, ba za a iya sanin inda za a yi amfani da su ba, don haka ya kamata a ɗauki waɗannan hare-hare a matsayin hare-hare ga al’ummar ƙasa baki ɗaya ba wai Jihar Yobe kaɗai ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Gwamna Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya ce bai dace a riƙa bai wa mutanen da suka wawure dukiyar ƙasa manyan muƙaman gwamnati kamar ministoci ba.

A cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Sanusi II, ya bayyana damuwarsa game da yadda ’yan Najeriya ke son dukiya fiye da gaskiya da tarbiyya.

Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC

Ya ce al’umma na girmama masu kuɗi, ko da kuwa an san kuɗin haram ne.

“Ƙasar da ke bai wa mutanen da aka san sun wawure dukiyar ƙasa muƙamin minista, za ta ci gaba da tafiya a doro mara kyau,” in ji Sanusi.

“Ba ma jin kunya idan wani ɗan siyasa ya tara dukiya ta hanyar da ba ta dace ba, sai ma mu yi masa tafi.”

Sanusi ya ce mutane da dama yanzu na shiga siyasa ne don su tara kuɗi, ba don su yi wa jama’a aiki ba.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan shugabanni suna auna darajarsu ne da adadin gidajen da suke da su, jiragen sama masu zaman kansu, ko kuɗaɗe a asusun banki.

Ya ce ba su damu da irin kyakkyawan tasirin da suka yi wa al’umma ba.

Ya kuma ce rashin tarbiyya da gaskiya a tsakanin shugabanni na ƙara raunana tsarin gwamnati gaba ɗaya.

A cewarsa, wasu ba su damu da abin da mutane za su ce game da su ba muddin sun mallaki dukiya.

Yayin da yake tunawa da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Murtala Muhammed, Sanusi ya ce Najeriya na buƙatar dawo da kyawawan ɗabi’u irin na shugabannin da suka gabace mu.

“Muna buƙatar daidaita ɗabi’unmu gaba ɗaya,” in ji shi.

“Ba wai shugaban ƙasa ko gwamnoni kaɗai ba ne za su canja ƙasa, kowa na da rawar da zai taka.”

Ya ƙara da cewa ’yan siyasa sun lalata tsarin aikin gwamnati, kuma Najeriya na buƙatar gina tsari mai ƙarfi da zai bai wa ma’aikatan gwamnati damar ƙin amincewa idan suka nemi su karya doka.

Sanusi, ya jaddada cewa kamata ya yi al’ummar Najeriya ta bai wa ɗabi’u kamar gaskiya, aiki tuƙuru, da tausayawa fifiko sama da tara dukiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II
  • Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya
  • Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
  • ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40
  • Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya
  • Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa