Aminiya:
2025-05-08@18:46:43 GMT

A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci – Ganduje

Published: 8th, May 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da shawarar yin amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan fashi a Nijeriya.

Shugaban ya bayar da shawarar ne a ranar Larabar da ta gabata a lokacin da ya jagoranci mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na ƙasa a ziyarar jaje ga gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a kan harin da aka kai wa rundunar sojijin barikin soja da ke Buni Gari.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’

Ganduje ya ce dole ne yaƙi da ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi da makami su tafi tare da haƙiƙanin lokaci domin samun nasara.

Ya bayyana cewa abin takaici ne irin yadda ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi suke aikata munanan ayyuka a faɗin ƙasar nan.

“A yanzu za a yi amfani da albarkatun da ake da su don maye gurbin irin kayan aikin da aka lalata.”

Da yake jawabi, gwamna Buni ya ce gwamnati a matakai daban-daban na duba yadda ake amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ‘yan ta’adda.

“Mu, a matakin ƙasa da gwamnonin yankin Tafkin Chadi, muna yin nazari sosai kan yadda maƙiya ke amfani da jirage marasa matuƙa aikata ta’assar wadda dole mu haɗa kai da jami’an tsaro don duba matsalar,” in ji Buni.

Ya ba da tabbacin cewa za a tattauna hakan a mataki mafi girma musamman da shugaban ƙasa domin daƙile ayyukan tada ƙayar baya da ’yan bindiga.

“Wannan matsala ce ta ƙasa domin a lokacin da suka kai hari a sansanin soji da kuma ƙwace makamai, ba za a iya sanin inda za a yi amfani da su ba, don haka ya kamata a ɗauki waɗannan hare-hare a matsayin hare-hare ga al’ummar ƙasa baki ɗaya ba wai Jihar Yobe kaɗai ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Gwamna Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi

A cewar sa, wannan bita tana da nufin tantance yadda aka samu cigaba a aiki, da kuma tabbatar da cewa hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar suna tafiya daidai da abin da aka ɗora masu a matsayin nauyi.

 

Ya ce: “Muna nan ne don sauraron shugabannin hukumomi domin mu ga yadda suka aiwatar da muhimman abubuwan da muka rattaba hannu a kai. Idan akwai ƙalubale, za mu tattauna su. Idan akwai cikas, za mu duba abin da za mu iya yi domin shawo kansu.”

 

Ministan ya bayyana wannan taro a matsayin hanyar tantance kai kafin a kai tsakiyar wa’adin gwamnatin yanzu.

 

Ya ce: “Ku tuna cewa wannan gwamnati ta fara aiki kusan shekaru biyu da suka gabata. Cikin ƙasa da wata guda daga yanzu, wannan gwamnati za ta kai rabin wa’adin ta a ranar 29 ga Mayu.

 

“Saboda haka, lokaci ya yi – kamar yadda Ofishin Shugaban Ƙasa ya nema – da kowace ma’aikata za ta fidda sakamakon aikin ta kan abubuwan da ta tsara kuma aka amince da su ta hannun ofishin CDCU da ke Ofishin Shugaban Ƙasa.”

 

Idris ya kuma jaddada cewa ma’aikatar sa na jajircewa wajen samar wa ‘yan Nijeriya da sahihan bayanai game da nasarorin gwamnati da kuma ƙalubalen da take fuskanta.

 

Ya ce: “Abin da wannan ma’aikatar ke yi shi ne tabbatar da cewa ba wai kawai muna wayar da kan ‘yan Nijeriya kan abubuwan da ke cikin hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba, har ma muna bayyana ƙalubalen da ke akwai cikin gaskiya da riƙon amana? Tabbas, wannan ne abin da muka ɗauka tun farko kuma za mu ci gaba da bin wannan hanya.”

 

Ya ƙara da cewa babban aikin ma’aikatar shi ne tsarawa da aiwatar da dabarun sadarwa masu ma’ana domin inganta gaskiya da rarraba bayanai game da manufofi da shirye-shiryen gwamnati, yaƙi da yaɗa ƙarya, da kuma ƙarfafa wayar da kan ‘yan ƙasa bisa fifikon gwamnatin Tinubu.

 

Taron ya samu halartar shugabannin hukumomi kamar haka: Darakta Janar na Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA), Kwamared Abdulhamid Dembos; Darakta Janar na Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Mista Lanre Issa Onilu; Darakta Janar na Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu; Darakta Janar na Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na Hukumar Kula da Tallace-tallace (ARCON), Dakta Olalekan Fadolapo; da Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
  • Almundahana: Jamiyar LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
  • Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
  • Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi
  • Ku Guji Rubuta Rahoton Farfagandar ‘Yan Ta’adda Mai Ɗaukar Hankali – Gwamnati Ga ‘Yan Jarida 
  • Jiragen Yaken HKI Sun Kai Hare-Hare A Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’aa Na Kasar Yemen
  • AU, ta yi tir da harin baya bayan nan a tashar ruwan Sudan
  • Dalilin Da Ya Sa Ɗan Sanda Ya Gyara Wa Ganduje Igiyar Takalmi – Hadimi
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa 50 A Yankin Zirin Gaza