Aminiya:
2025-08-07@12:50:03 GMT

Ficewar ’yan majalisa 3 a PDP: Raɗɗa ya halarci zauren majalisar Wakilai

Published: 8th, May 2025 GMT

Da safiyar Alhamis ɗin nan ne Gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa ya halarci zauren Majalissar Wakillai ta ƙasa domin sheda ficewar Ƴan Majalissa uku na Jihar Katsina daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC

Ƴan majalissar sun haɗa da Ɗan majalisa mai wakiltar (Mashi/Dutse) Hon. Salisu Yusuf Majigiri, da na (Bakori/Ɗanja) Hon.

Abdullahi Balarabe Dabai, sai na (Batsari/Safana/Ɗanmusa) Hon. Iliyasu Abubakar.

An kama mutum 6 da ake zargi kan garkuwa da mutane A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci — Ganduje

Gwamnan Raɗɗa ya taya ’yan majalissar murnar dawowa cikin Jama’iyyar APC, wanda dawowar su jam’iyyar ya nuna irin haɗin kai da jam’iyyar take da shi a Jihar Katsina.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai

Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai

Wata kungiyar matasa, Kauru Youth Ambassadors (KYA) a karamar hukumar Kauru sun nuna matukar damuwa kan yadda Barnabas Danmaigona, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kauru a majalisar dokokin jihar Kaduna, ya gaza samar da ingantaccen wakilci tun bayan zaben sa.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai taken daga ‘Daga Fata zuwa Yaudara’ wanda kuma Junaidu Ishaq Maisalati, ya sanyawa hannu, kungiyar ta caccaki dan majalisar kan abin da ta bayyana a matsayin mai dimama kujera kuma ɗan siyasar da ya gaza wajen gudanar da ayukka a mazabar da kuma aikin da zai amfani al’umma.

Sanarwar ta koka da yadda al’ummar Kauru suka sanya kyakkyawan fata a shugabancin Danmaigona, amma a maimakon haka, ya kasa ba marada kunya.

Har ila yau, ta yi Allah-wadai da kawancen siyasarsa da Mukhtar Chawai, wani dan siyasa da aka ce ko ake zargin baya tabuka komai a mazabarsa ba, tare da bayyana cewa irin wannan kawancen yana kashe musu gwiwa matukar gaske.

KYA ta bayyana rashin jin dadin ta a kan abin da suka kira wasu ‘yan kudaden da basu gaza dubu 5 zuwa 10 da yake rabawa jama’a a matsayin yankawa kare ciyawa domin wannan ba abin da suke tsinanawa al’ummar da yake wakilta

Saboda haka Kungiyar ta bukaci al’ummar mazabar Kauru da su tashi tsaye akan nuna halin ko-in-kula a siyasance, su nemi wakilcin da ya dace, sannan su ki yarda a ba su kyauta irin wannan da bata tsinana musu komai.

Sun yi nuni da ‘yan majalisa irin su Hon. Shehu Yunusa na Kubau, wanda rahotanni suka ce ya ba da fifiko wajen hada kai da ci gaba, a matsayin misalan yadda wakilci na gaskiya ya kasance.

Da take kira da a wayar da kan ‘yan siyasa da kuma daukar matakin gama gari, sanarwar ta kalubalanci matasa da masu kada kuri’a a Kauru da su yi wa shugabanninsu hisabi, inda ta dage cewa zabe aiki ne..

KYA ta bayyana cewa Hon. Danmaigona ya samu damarsa, kuma har yanzu jama’a na nan suna jira, ba wai kawai alkawura ba, a’a, a samu canji na zahiri.

Rel/Yusuf Zubairu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Tataba
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
  • Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru
  • Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara