Aminiya:
2025-05-08@21:13:30 GMT

Ficewar ’yan majalisa 3 a PDP: Raɗɗa ya halarci zauren majalisar Wakilai

Published: 8th, May 2025 GMT

Da safiyar Alhamis ɗin nan ne Gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa ya halarci zauren Majalissar Wakillai ta ƙasa domin sheda ficewar Ƴan Majalissa uku na Jihar Katsina daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC

Ƴan majalissar sun haɗa da Ɗan majalisa mai wakiltar (Mashi/Dutse) Hon. Salisu Yusuf Majigiri, da na (Bakori/Ɗanja) Hon.

Abdullahi Balarabe Dabai, sai na (Batsari/Safana/Ɗanmusa) Hon. Iliyasu Abubakar.

An kama mutum 6 da ake zargi kan garkuwa da mutane A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci — Ganduje

Gwamnan Raɗɗa ya taya ’yan majalissar murnar dawowa cikin Jama’iyyar APC, wanda dawowar su jam’iyyar ya nuna irin haɗin kai da jam’iyyar take da shi a Jihar Katsina.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya yi zargin cewa sojoji da sauran jami’an tsaro na bayar da gudunmawar aikata miyagun laifuka da cin zarafin jama’a a Nijeriya.

Zulum ya faɗi hakan ne yayin da yake haramta sayar da barasa a birnin Maiduguri da kewaye.

Ka-ce-na-cen da ya biyo bayan ziyarar Tinubu a Katsina DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A Najeriya

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Talata a wajen ƙaddamar da wani kwamitin da aka kafa don “ƙwace haramtattun otal-otal da gidajen karuwai da gidajen kwana da maɓoyar miyagun laifuka da kuma daƙile illolin munanan ɗabi’u.

Gwamnan ya ce tsofaffin jami’an tsaron Nijeriya da na yanzu da suke aiki sun taka rawa wajen jawo jama’a cikin aikata miyagun laifuka kamar tsaurin ra’ayi da karuwanci da sauran munanan ɗabi’u, lamarin da ke kara ta’azzara barazanar ta’addanci a jihar.

“Na yi farin ciki da sanin cewa jami’an soji suna wajen nan, musamman sojoji, ‘yan sanda, da sauran su, domin yawancin waɗannan ayyukan wa ke yin su?

“Wasu daga cikinsu akwai jami’an soji da aka kora da masu ci a yanzu har da fararen hula.

“Don haka, bai kamata a ƙi sukar kowane ɓangare ba a cikin wannan lamarin idan har muna son babban birnin Maiduguri da kuma jihar ta kawar da ta’addanci da sauran laifuka,” in ji Zulum.

A takaitaccen taron, Zulum ya sake kafa kwamitin tare da sake ba wa kwamitin damar kawar da duk wani nau’i na miyagun laifuka da munanan ɗabi’u a cikin birnin Maiduguri da kewaye.

Dokar hana sayar da barasa da kayan maye, a cewar gwamnan, ta samo asali ne daga yadda ake ta samun tashe-tashen hankula a tsakanin ƙungiyoyin da ke gaba da juna da ƙungiyoyin asiri da karuwanci da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ‘yan fashi da sata, waɗanda suka haddasa asarar rayuka da dukiya.

Gwamnan ya haɗa hannu da sojoji, ‘yan sanda, sibil difens da wasu jami’an tsaro da dama da suka haɗa da ’yan sa-kai domin shiga cikin kwamitin domin gudanar da cikakken bincike.

Da yake amincewa da aikin da ke gaban kwamitin da aka sake kafawa, shugaban kwamitin ya yi tir da tabarbarewar harkokin tsaron cikin gida a Maiduguri tare da bayyana matakin da kwamitin zai ɗauka nan take.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Buni ya tallafawa iyalan sojojin da suka mutu 
  • An Tabbatar Da Ficewar Sanata Sumaila Daga NNPP Zuwa APC A Majalisa
  • Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum
  • Ka-ce-na-cen da ya biyo bayan ziyarar Tinubu a Katsina
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Zartas da Dokar Sabon Kudiri Kan Kwalejin Nuhu Bamalli, Ta Soke Na 1989
  • Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas
  • Gwamnan Bauchi Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Banga A Alkaleri
  • Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus
  • Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsina