Aminiya:
2025-12-10@20:31:11 GMT

Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura

Published: 15th, April 2025 GMT

Wani ƙazamin rikici da ya janyo salwantar rayukan fiye da mutum 50 a Jihar Filato ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya.

Aƙalla mutane 51 ne aka kashe a wasu hare-hare biyu da aka kai a yammacin Lahadi a Jihar Filato da ke Arewa maso tsakiyar Nijeriya.

Mahukunta a Filato sun ce an kai harin ne a cikin daren Litinin a garin Zike da ke yankin Kwall a Ƙaramar Hukumar ta Bassa.

Mai bai gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Admiral Shipi Gakji mai ritaya, ya tabbatar wa BBC cewa an kai harin ne a cikin dare, wayewar garin Litinin kuma adadin waɗanda aka kashe “ya zarce 40.”

Sai dai Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar ta Filato ta tabbatar wa BBC cewa adadin waɗanda suka rasa rayukansu a harin ya kai mutum 51.

“Maharan sun shiga ne suka buɗe wuta ne kan mutane suna barci suka ji ruwan harsasai.

“Sun kashe mutane a gidaje da kuma kan titi, yanzu an ƙidaya gawarwaki 51, in ji Sunday Abdu, Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Filato.

Bayanai sun ce wasu mahara ɗauke da makamai ne suka yi harbin kan mai uwa da wabi a ƙauyukan Zike da Kimakpa, inda nan take mutane 47 suka mutu, yayin da wasu 22 suka jikkata waɗanda aka kwantar da su a asibiti.

Wannan hari ya zo ne kwanaki 10 bayan tashin hankalin da ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40 a yankin.

Dole a ɗauki mataki — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah wadai da ƙazamin harin, yana mai kira Gwamna Caleb Mutfwang da ya ɗauki matakin magance matsalar da ake samu.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Shugaban ya aike da saƙon jaje ga gwamnatin Jihar Filato da kuma jama’ar jihar, tare da kiran gwamnan jihar da ya ɗauki matakan da suka dace na siyasa wajen warware rikicin da kuma samar da dawwamammen zaman lafiya.

Yayin da yake bayani kan muhimmancin zaman lafiya a tsakanin al’ummar jihar, Tinubu ya buƙaci son juna da haɗin kai ba tare da nuna banbancin ƙabila ko kuma addini ba.

Shugaban ya buƙaci shugabannin addinai da na siaysa a ciki da wajen jihar da su haɗa kai wajen kawo ƙarshen irin waɗannan hare hare da kuma ɗaukar fansar da ake gani, waɗanda ke jefa al’ummomi cikin tashin hankali.

Tinubu ya ce ya zama dole rikicin Filato da ya samo assali daga rashin fahimtar juna tsakanin kabilu da kuma addinai ya zo ƙarshe, yayin da ya ce ya umarci hukumomin tsaro da su gudanar da bincike na haƙiƙa domin gano waɗanda ke ɗaukar alhakin rikicin domin gwamnatinsa ba za ta amince da hare-haren ramakon ba.

Baya ga hukunta waɗanda suke da hannu a rikicin, shugaban ya ce ya zama dole ga shugabannin siyasar jihar, a ƙarƙashin Gwamna Caleb Mutfwang da su magance assalin rikicin dake tsakanin jama’a.

Tinubu ya ce wannan rikici na tsakanin al’umma na sama da shekaru 20, kuma ba za a iya kaucewa dalilan da ke haifar da su ba, don haka ya zama wajibi a tinkare su ta hanyar adalci.

Cikin waɗanda aka kashe har da yara da tsofaffi — Amnesty

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta Amnesty International ta yi kakkausan Allah wadai da kisan aƙalla mutum 51sakamakon harin ‘yan bindiga suka kai ƙauyen Zikke.

Amnesty ta koka kan cewa da yawan waɗanda abin ya shafa sun kasa tserewa — ciki har da yara da tsofaffi — wanda sakamakon hakan ‘yan bindigar suka yi musu kisan gilla suka bar su cikin jini kace-kace.

“Dole ne a binciki gazawar hukumomi kuma a daina yi musu uzuri saboda yadda wasarere din da suke yi wa sha’anin tsaro ke haifar da waɗannan munanan hare-hare, makonni biyu bayan kashe mutum 52,” in ji Amnesty.

Ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam ɗin ta ƙara da cewa “yin Allah kawai da wadannan munanan hare-haren bai wadatar ba kuma dole ne a nuna jajircewar kare al’umma ta hanyar tabbatar da adalci.

“A yayin da Shugaba Tinubu ke ikirarin cewa gwamnatinsa tana sanya sabbin matakan tsaro don magance ƙaruwar rashin tsaro a ƙasar, hare-hare na bayan nan a jihar Filato na nuna cewa dukkan matakan tsaron da ake ɗauka ba sa aiki,” ta ce.

Ƙungiyar ta ba da alkaluma na yawan mutanen da aka kashe a Jihar Filato daga Disamban 2023 zuwa Fabrairun 2024, inda ta ce an kashe mutum 1,336.

Daga cikin wadanda aka kashe 533 mata ne sai yara 263, sannan maza manya 540.

Kazalika ta ce fiye da mutum 29,554 ne suka rasa matsugunansu, daga cikinsu 13,093 yara ne yayin da mata 16,461 suka rasa matsugunansu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Filato a jihar Filato a Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.

ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.

Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.

Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.

Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.

Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.

A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.

Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”

ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.

Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.

Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso