Aminiya:
2025-09-18@00:39:08 GMT

Babu ɗaya daga cikin buƙatunmu da gwamnati ta aiwatar — Shugaban ASUU

Published: 27th, August 2025 GMT

Shugaban Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), Farfesa Chris Piwuna, ya ce Gwamnatin Tarayya ba ta aiwatar da ɗaya daga cikin yarjejeniyar da ta ƙulla da ƙungiyar ba.

Ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin hira da gidan talabijin na Trust TV.

’Yan bindiga sun sace ma’aurata da ’yarsu mai shekara ɗaya a Katsina DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Farfesa Piwuna, ya ce ASUU a koyaushe na zaɓar tattaunawa da jami’an gwamnati a matsayin mafita.

Amma duk da cewa sun cimma matsaya kan batutuwa masu muhimmanci kamar kuɗaɗen gudanarwa, albashi, ’yancin malamai, ‘yancin jami’o’i, da sake duba wasu dokoki, ba a ɗauki mataki kan kowanne ba.

“Babu saɓani a tsakaninmu da tawagar gwamnati,” in ji shi.

“Mun amince kan abubuwa da dama, sai dai shugabanninsu, Ma’aikatar Ilimi da Gwamnatin Tarayya ba su ɗauki mataki kan kowanne ba.”

Ya danganta yawan ficewa daga Najeriya da malamai da likitoci ke yi saboda ƙarancin albashi da mummunan yanayi da suke ciki.

A asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos inda yake aiki, ya ce aƙalla likitoci 20 sun bar aiki cikin shekara biyu.

“Yanayin daidai yake da na malaman jami’a. Idan ƙarancin albashi ne ke sa mutane barin aiki, me ya sa ba za a ƙara albashi a riƙe su ba?” ya tambaya.

Ya ƙara da cewa ƙasashe da dama a Afirka suna ɗaukar malaman Najeriya aiki.

“A Uganda, a cikin jami’a guda ɗaya za ka iya samun malamai ’yan Najeriya sun kai 20,” in ji shi.

Shugaban ASUU ya kuma nuna damuwa kan mummunan yanayin kayan aiki a jami’o’in Najeriya, inda ya ce hakan na daga cikin dalilan da ya sa ba sa samun matsayi mai kyau a duniya.

Ya ce daga cikin jami’o’i 333 da faɗin Najeriya, guda biyar ne kaɗai ke cikin jirin manyan jami’o’i 1,000 a nahiyar Afirka.

Ya ce malamai ba sa jin daɗin tafiya yajin aiki, amma gwamnati na tilasta musu hakan saboda rashin ɗaukar mataki.

“Yajin aiki yana shafarmu, iyalanmu, da ɗalibanmu. Amma idan gwamnati ba ta yi komai ba, harkar ilimi za ta ci gaba da taɓarɓarewa.”

Ya yi kira ga kafafen yada labarai, iyaye, ƙungiyoyi, sarakuna da shugabannin addinai da su haɗa kai wajen nema wa ɓangaren ilimi sauyi a Najeriya.

“Wannan ba batun ASUU ne kaɗai ba. Muna fafutukar samun ingantaccen tsari ne, da kyakkyawar makoma, da kuma alheri ga ƙasarmu,” a cewarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gwamnatin tarayya Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.

Ministan Noma  Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta  Jihar Jigawa.

 

Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.

Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.

Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na  zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.

Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa