Aminiya:
2025-12-14@07:20:02 GMT

Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar

Published: 15th, April 2025 GMT

Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.

Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.

TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.

Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.

Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.

An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.

Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.

Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakarun tsaron yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba

Gwamnatin Jamhuriyar Benin, ta fitar da sammacin kame dan fafatukar nan Kemi Seba da ya shahawa wajen kalubalantar siyasar faransa a kasashen Afrika.

Matakin dai an zuwa ne kasa da mako guda bayan yunkurin juyin mulki da aka yi wa Shugaba Patrice Talon, wanda ya girgizar kasar.

Kotun Jamhuriyar Benin ta bayar da sammacin kama, Kemi Seba da Sabi Sira Korogone, shugaban kungiyar ‘Yantar da Jama’a (MPL), bisa zargin goyan bayan ayyukan ta’addanci” da kuma “tunzura mutane su yi bore.”

Mutanen biyu za su iya fuskantar hukuncin daurin shekaru biyu zuwa biyar a gidan yari da kuma tarar miliyan goma na CFA, a cewar wata majiyar shari’a.

Shi dai Kemi Seba, ya fitar wani bidiyo a ranar 7 ga Disamba inda ya yi murna da yunkurin juyin mulkin da aka yi wa shugaba Patrice Talon.

A cikin bidiyon, dan fafutukar ya yi nuni da wani yunkuri na farko da za a iya maimaitawa idan shugaban kasar bai sake duba ayyukansa ba, wanda hakan ya haifar da fushi daga hukumomi.

A lokaci guda kuma, an kama Candide Azannaï, tsohon Ministan Tsaro kuma babban jigo a jam’iyyar adawa, a safiyar Juma’a a Cotonou.

An kama shi ne a hedikwatar jam’iyyarsa, inda ‘yan sandan shari’a ke yi masa tambayoyi.

A yanzu haka, ba a fayyace ainihin dalilan kama shi ba. Duk da haka, Azannaï ya nisanta kansa daga juyin mulkin da bai yi nasara ba na ranar 7 ga Disamba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan December 12, 2025 Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  •  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahadi A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran