Aminiya:
2025-12-11@23:52:21 GMT

Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar

Published: 15th, April 2025 GMT

Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.

Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.

TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.

Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.

Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.

An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.

Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.

Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakarun tsaron yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi

An kori direban Kamfanin Simintin Mangal bayan jami’an tsaro sun kama shi da motar kamfanin dauke da yara 21 da ake zargin an yi safarar su ne daga jihohin Arewa.

Gwamnatin jihar ta ce yaran da ke tsakanin shekaru 6 zuwa 17 an kama su ne bisa sahihan bayanan sirri.

Sanawar da Kwamishinan Yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar bayan kama yaran a cikin motar ta yi zargin za a yi amfani da su wajen horar da ’yan ta’adda.

Kamfanin ya nesanta kansa daga lamarin, ya ce direban ya karya dokokin aiki, kuma ya jefa al’umma cikin haɗari.

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Babban Manajan sashin kula da mulki na kamfanin, Musa Umar, ya ce ba da izininsa direban da aka kama ya fita da motar ba, domin iya jigilar siminta kaɗai suke yi ba ɗaukar fasinja ko yara ba.

Gwamnatin Kogi ta ce za a mika yaran ga gwamnatocin jihohinsu bayan tantancewa, yayin da duk wanda aka samu da hannu a safarar zai fuskanci shari’a bisa dokokin hana safarar yara da kare haƙƙin yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahadi A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi