Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
Published: 15th, April 2025 GMT
Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.
Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.
Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.
TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.
Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.
Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.
An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.
Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.
Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakarun tsaron yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
Wani magidanci tare da ɗaukacin iyalinsa huɗu sun rasu sakamakon wata gobara da ta tashi a sanadin kunna maganin sauro a layin Baba Impossible da ke Unguwar Kundila, da ke Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da tashin wutar da misalin ƙarfe 4:13 na Asubar ranar Laraba.
NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar AnsaruMai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce sun samu kiran wani ma’aikacinsu, HFS Abba Datti, game da gobarar.
A cewarsa ba tare da ɓata lokaci ba suka tura jami’ansu daga hedikwatar hukumar zuwa wajen da gobarar ta tashi.
“Lokacin da muka isa, mun ga wani gida mai girman ƙafa 40 da 30 yana ƙone gaba ɗaya. Gobarar ta shafi ɗakuna biyu, falo, bayan gida, da kuma ɗakin girki,” in ji sanarwar.
Mutane biyar ne gobarar ta rutsa da su; mai gidan mai suna Shodandi mai shekara 43, matarsa Rafi’a mai shekara 30.
Ragowar kuma ’ya’yansu ne; Mardiya Shodandi mai shekara uku, Yusira Shodandi ’yar shekara ɗaya da rabi da Aminu Shodandi ɗan watanni 12.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Huɗu daga cikinsu; uba, uwa, da ƙananan yara biyu sun ƙone kafin a ceto su. Amma an samu damar ceto Aminu ɗan watanni 12.”
Hukumar ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ga iyalan mamatan, ta kuma ta gargaɗi mutane da suke kula sosai, musamman a lokacin sanyi.
Bincike ya nuna cewa gobarar ta samo asali ne daga maganin sauro da matatan suka kunna a falo, sannan suka yi barci.