Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
Published: 15th, April 2025 GMT
Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.
Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.
Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.
TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.
Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.
Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.
An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.
Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.
Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakarun tsaron yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
’Yan sanda sun kama tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji Rimin Gado.
Rahotanni sun nuna cewar wasu ’yan sanda ɗauke makamai ne suka kama shi a ofishinsa da ke Kano, bayan tafka jayayya a ranar Juma’a.
Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026 Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — ZulumWaɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun ce manyan motocin ’yan sanda cike da jami’an da ke ɗauke da makamai ne suka dira ofishinsa da ke kan titin zuwa Zariya.
Sun gargaɗi mutane da kada kowa ya kusanci ofishin, inda suka yi barazanar buɗe wa duk wanda ya yi yunƙurin tsoma baki a lamarin wuta.
Muhuyi, ya nemi jami’an su nuna masa takardar kama shi ko su bayyana dalilin kama shi.
Sai dai jami’an sun ƙi bayyana komai, face cewar umarni aka ba su daga Hedikwatar ’Yan Sanda ta Ƙasa da ke Abuja.
Lauya Ridwan Zakariyya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce bayan tafka jayayya, daga bisani an kai Muhuyi hedikwatar ’yan sanda ta Kano da ke Bompai.
Ya ce jami’an sun ce su wani rukuni ne na musamman na Sufeto Janar na ’Yan Sanda da aka aiko daga Abuja.
Zakariyya, ya ƙara da cewa jami’an sun yi yunƙurin ƙwace wayar Muhuyi tare da yin barazanar harbi.
Wannan shi ne karo na biyu da ake kama Muhuyi a shekarar 2025.
A farkon watan Janairu, rundunar IGP Monitoring Unit ta kama shi kan almundahanar wasu kuɗaɗe da ake zargin suna da alaƙa da wani jigo na jam’iyyar APC, amma daga baya aka sake shi.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, CSP Abdullahi Kiyawa, ya ci tura, domin bai amsa wayarsa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.