HausaTv:
2025-11-26@13:53:59 GMT

Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin

Published: 14th, April 2025 GMT

Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.

Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.

‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.

Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.

A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.

A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.

Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.

A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila

Daga Musa kutama , kalaba
Hasana Aminu matashiyar jaruma ce a Masana’antar Kannywood, wacce ta fito a finafina da dama ciki har da fim xin A Duniya da wasu fitattun finafunan Hausa. A zantawarta da Aminiya, Hasana Aminu wadda aka fi sani da suna Nabila ta ce, a halin yanzu tana tauna taura biyu ne a baka
Ga yadda girar su ta kasan ce:
Sunan Jarumar?
Sunana Hasana Aminu, amma an fi sani na da suna Nabila a Masana’antar Kannywood da ke Kano
Ta yaya kike gwama karatu da kuma kasuwanci da harkar fim?
Eh, to farko ko da na shigo Masana’antar Kannywood sai na ga ai ashe ma ina da damar da zan iya yin karatu yayin da kuma nake sana’ata ta harkar fim. Domin kafin in fara fim na riga na samu kwalina na NCE. To sai na fahimci tunda dai ban da harkar fim kuma ina yin kasuwancin da zai iya taimaka min in xauki nauyin qaro karatu, ai gara in je in karo karatun. Wannan ne dalilin da ya sa na koma karatu, inda yanzu nake karatun Kimiyyar Aikin Xakin Gwaje-gwaje a matakin Babbar Difloma wato HND kuma sakamakon haka wasu ma daga cikin ‘yan masana’antar sun yi koyi da ni, sun koma makaranta su ma suna ci gaba da karatunsu.
Yi wa mai karatu bayanin yadda kika gwama karatun fim da kuma kasuwancu?
Gaskiya daga Asabar zuwa Lahadi ne nake zuwa karatun, daga Litininn zuwa Juma’a duk ina da lokaci da nake tafiya harkokin fim xin.
Don yanzu duk a inda aka kira ni a harkar fim ina da lokacin da zan je in dawo tsakanin Litinin zuwa Juma’a. Amma Asabar da Lahadi kowa ya san ranar makaranta ce duk wanda ke masana’antar ko ya aiko ya san lokacin makaranta ne.
Ko hakan bai sanya kin takura kanki ba?
Gaskiya ban tava jin na takura kaina ba, wani abin ma da ya fi haka duk zan iya haxawa da shi saboda ina da lokaci isasshe.
Ga wanda duk ya karanta wannan hira ta yaya zai iya gane cewa Hasana Aminu ce ta Kannywood da ake kallo a fim xin kannywood?
Eh, duk wanda ya san ni ko ya kalli finafinan da na yi kamar su Dare Xaya da Rigar Aro zai san ni ce
Ki fito a fim xin Xan Jarida kuma a matsayin ‘yar jarida kika fito, ko a iya cewa ke ma hala kina da shauqin zama ‘yar jarida ?
A gaskiya na fito dai a qanwar xan jaridar, inda na kasance abokiyar shawararsa a kan duk abin da yake yi ya riqa taqaitawa a irin aikinsa da kuma duk abin da yake yi ya lura da aikinsa.
Ko hakan ta sa ke ma kina sha’awar aikin jarida?
(Dariya) gaskiya ba na da sha’awar hakan.
Waje xaya ana samun wasu ‘yan matsaloli a Kannywood ta yadda ake samun ta da qura tsakaninsu da hukumomi, sai ga shi wasu kuma yanzu ne ma suke shirin shigowa masana’antar. Me za ki ce?
To gaskiya matsala kam akwai ta masu qoqarin shigowa kada su daka ta wasu waxanda suke ciki. Domin kowa da irin tarbiyarsa. Sannan kuma su yi binciken mutanen da suke son su shigo ta hannunsu
Batun manyan matoci na alfarma da riqe manyan wayoyi da mutane ke yawan ta da qura suna baza zarge-zarge ga ‘yan fim musamman mata. Me za ki ce?
Eh to idan duba wani lokaci za ka ga wani abu shi ke ta da wani. Domin in ka yi la’akari da hawa babbar mota, ai akwai maza akwai mata a Masana’antar Kannywood kuma matan ne kawai aka fi zargin gani suna hawa motocin. To su mazan me ya sa ba su hawan manyan motocin ko su ba su samun kuxi ne kamar mazan. Don haka wannan ba abu ne da zan so zurfafawa ba domin idan ka shigo harkar Kannywood za ka ga abubuwa da daman gaske. Kuma a rayuwa idan mutum bai da damar yin abu kuma ya sa wa kansa dole sai ya yi shi ko ta wane hali, to za a iya shiga wani hali da ba a zata ba.
Sabon salon xora finafinai a YouTube da haskawa a sinimar hakan ko a ganinki ya kawo wani ci gaba?
Eh, to wannan ka ga shi yanayin harkar ce abu ne wanda su masu shirya fim suke dubawa, ka ga mutum a da zai iya ya sayar da fim xinsa na series wato mai dogon zango, amma a yanzu yana da dama biyu ta xorawa a YouTube da sayarwa don samun riba.
Ana samun karvuwar finafinan Hausa a sauran qasashe maqwabtan Nijeriya. Me za ki ce a kan haka musamman a qasashen Nijar da Kamaru Ghana da Chadi ?
Gaskiya hakan na faruwa ne saboda yadda ake inganta ayyukan fim a Kannywood ta hanyar qwarewa da kuma samar da ingantattun kayan aiki. Wato lokaci ne kowa ya sa kuxinsa zai ga kuxinsa yadda ka zuba kuxi, ka yi fim hakan za ka ga ya yi gaba zuwa wasu wuraren da ma ba ka yi tsammani ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi