HausaTv:
2025-12-06@14:56:14 GMT

Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin

Published: 14th, April 2025 GMT

Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.

Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.

‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.

Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.

A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.

A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.

Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.

A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta ce Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi

Mataimakin kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ya gargadi Amurka da kawayenta game da tsaron tekun fasha da mashigar Hurmuz, yace tsaron wadannan muhimman wurare jan layi ne ga kasar iran da zata mayar da martani mai tsanin ga duk wanda ya taba su

Brigadier Janal Ali Fadavi da yake bayani game da muhimmancin mashigar Hurmuz ya fadi cewa babu wata yarjejeniya da za’a yi game da samun tabbaci ga makamashi na duniya, inda sama da ganga miliya 20 take wucewa ta wannan mashigar kullum , kuma duniya ta dogara ne da makamashin na tekun fasha

Janar fadavi ya bayyana cewa dakarun kare juyin musulunci na kasar iran sun shirya tsaf wajen kare wannan yankin mai muhimmanci da dukkan karfi, a bangaren ruwa ne ko kuma ta sararin samaniya idan makiya suka yi barazana ga tsaronmu to zamu tunkaresu da dukkan karfinmu.

Yayi Allah wadai da ayyukan ta’addanci da Amurka da isra’ila ke yi kuma ya bayyanasu a matsayin manyan wadanda ke tada zaune tsaye a duniya daga tekun fasha har zuwa yankin latin Amurka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta  Kama Olmert Da Livni December 4, 2025 Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaron kasar December 4, 2025 Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka December 3, 2025 MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI December 3, 2025 An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha
  •  Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya
  • Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin  Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Yankin Gaza
  • Iran Ta ce Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi
  • Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai