Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
Published: 14th, April 2025 GMT
Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.
Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.
‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.
Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.
A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.
A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.
Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.
A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta tabbatar da mutuwar wasu jami’anta guda biyar a ƙauyen Sabon Sara da ke Ƙaramar Hukumar Darazo, sakamakon harin da wasu ’yan bindiga suka kai.
Kakakin rundunar, CSP Ahmed Wakil ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranae Lahadi.
An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu Ɗalibai 50 da aka sace a Neja sun kuɓuta — CAN“‘Yan sanda biyar sun rasu, biyu sun jikkata, amma an yi nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar a ƙauyen Sabon Sara, Ƙaramar Hukumar Darazo, a jihar Bauchi.”
Wakil, ya ƙara da cewa, “Ma’aikatanmu suna jajircewa kuma sun samu nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar yayin musayar wuta.”
Ya bayyana ’yan sanda suna aikin sintiri lokacin da aka kai musu harin.
Wakil, ya bayyana sunayen ’yan sandan da suka rasa rayukansu; DSP Ahmad Muhammad (SID), ASP Mustapha Muhammad (10 PMF), Amarhel Yunusa (10 PMF), Idris Ahmed (10 PMF), da Kofur Isah Muazu (AKU).
’Yan sandan da suka ji rauni sun haɗa da Isah Musa (SID) da Insifekta Yusuf Gambo (SID).
Ya ƙara da cewa, “Bayan samun rahoton, Shugaban ’yan sandan Ƙaramar Hukumar, SP Auwalu Ilu, ya jagoranci tawaga tare da ceto waɗanda suka jikkata.
“Sun kai waɗanda suka rasu Babban Asibitin Darazo, inda aka ajiye gawarwakin a ɗakin ajiyar gawa.
“Ana ƙokarin kama waɗanda suka aikata wannan mummunan laifi tare da hukunta su,” in ji Wakil.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya ziyarci wajen da lamarin ya faru, sannan miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.
“Aikin nan ba abu ne mai sauƙi ba. Duk da haka, bisa doka, za mu ci gaba da jajircewa ba dare ba rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.”