Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
Published: 14th, April 2025 GMT
Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.
Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.
‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.
Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.
A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.
A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.
Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.
A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
Gwamnatin Jihar Kwara ta bayar da umarnin rufe makarantu a ƙananan hukumomin jihar guda huɗu na saboda ƙaruwar hare-hare a jihar cikin sa’o’i 48 da suka gabata.
Aƙalla mutane uku sun mutu a garin Bokungi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a ranar Laraba.
Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan AmurkaLamarin ya faru kasa da sa’o’i 24 bayan mummunan harin da aka kai coci a Eruku, Ƙaramar Hukumar Ekiti ta jihar, inda aka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da mutum 30.
Majiyoyin al’umma sun ce an fara yin garkuwa da mutane huɗu, ciki har da ɗan sa-kai, a cikin waɗannan hare-haren.
Ɗaya daga cikin majiyoyin ya ce maharan daga baya sun kashe manoman shinkafa biyu tare da jikkata wani mutum na uku wanda aka ce ɗan sa-kai ne.
A halin yanzu, gwamnati ta ce ta ɗauki matakan tsaro na musamman a makarantu, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinta na tabbatar da kariya ga ɗalibai.
Matakan dai sun shafi makarantu a ƙananan hukumomin Ifelodun, Ekiti, Irepodun, Isin, da Oke Ero.
Gwamnatin ta ce wannan mataki ya nuna ƙudurinta na dakile ayyukan masu garkuwa da mutane waɗanda za su iya amfani da ɗalibai a matsayin garkuwa daga matsin lambar da suke fuskanta.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi da Ci gaban Ɗan Adam na jihar, Dr Lawal Olohungbebe, ya fitar, ya ce matakan sun shafi makarantun kwana a Irepodun.
Sanarwar ta ƙara da cewa matakin zai ci gaba da kasancewa a yankunan har sai an samu cikakken tabbacin tsaro kafin a dawo da harkokin yau da kullum.
A ranar Litinin, ’yan bindiga sun kai hari a makarantar GGCSS Maga, Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu ta Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum ɗaya tare da yin garkuwa da ɗalibai 25.