HausaTv:
2025-11-25@11:30:43 GMT

Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin

Published: 14th, April 2025 GMT

Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.

Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.

‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.

Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.

A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.

A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.

Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.

A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza sau 500 cikin kwanaki 44

Ofishin Yada Labarai na Gwamnatin Gaza ya ce Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza da Amurka ta shiga tsakani akalla sau 497 cikin kwanaki 44, inda ta kashe daruruwan Falasdinawa tun lokacin da yarjejeniyar ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba.

Ofishin ya ce Isra’ila ce ke da alhakin dukkan tabarbarewar al’amuran jin kai da tsaro sakamakon keta yarjejeniyar tsagaita wuta da ta yi akai-akai.

An kashe fararen hula 342 a hare-haren, mafi yawansu yara, mata da tsofaffi ne.

“Muna Allah wadai da ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta mai tsanani da aka yi da hukumomin mamayar Isra’ila,” in ji ofishin a cikin wata sanarwa.

Isra’ila ta ci gaba da takaita kwararar kayan agaji da magunguna cikin yankin da aka lalata kamar yadda aka tsara a cikin yarjejeniyar tsagaita wuta.

Sojojin Isra’ila sun kai hare-hare ta sama a fadin Gaza a ranar Asabar, inda suka kashe akalla Falasdinawa 24, ciki har da yara.

Ofishin Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce sun kai hare-haren na baya-bayan nan ne bayan wani mayakin Hamas ya kai hari kan sojojin Isra’ila a yankin da Isra’ila ta mamaye a layin rawaya na Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu November 23, 2025 ‘Yan Isra’ila na neman a gudanar da bincike kan harin ranar 7 ga Oktoba November 23, 2025 An  Cimma Yarjejeniya A Karshen Taron Kare Muhalli Na Duniya A Kasar Brazil November 23, 2025 Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci November 23, 2025 An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba November 23, 2025  An Kulla Yarjejeniyar Aikin Soja A Tsakanin Kasashen UAE Da Ethiopia November 23, 2025 Pezeshkian: Iran na Allawadai da hare-haren Isra’ila a kan Lebanon November 23, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161 November 23, 2025 Esma’il Khatib: Isra’ila Na Fuskantar Manyan Ayyukan Leken Asiri Daga Iran November 23, 2025 An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka November 23, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza sau 500 cikin kwanaki 44
  • Isra’ila Ta Kashe Yara Falasdinawa Guda 22 A Yankin Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba