HausaTv:
2025-12-12@06:17:38 GMT

Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin

Published: 14th, April 2025 GMT

Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.

Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.

‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.

Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.

A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.

A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.

Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.

A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan: Reuters

Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump ta bukaci kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) ta yi gyara ga yarjejeniyar da aka kafa domin kare Trump da manyan jami’an Amurka daga duk wani bincike na yanzu ko nan gaba, in ji wani jami’in gwamnatin Trump a ranar Laraba. Barazanar dai na kunshe ne da gargadin kara sanya takunkumi idan kotun ta ki bin umarnin.

Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, wa’adin na Washington ya hada da karin wasu bukatu guda biyu: cewa kotun ta ICC ta janye bincikenta kan laifukan yaki da shugabannin Isra’ila suka aikata a lokacin yakin Gaza, da kuma cewa ta rufe binciken da ta yi tun farko kan halin sojan Amurka a Afghanistan. Idan kotu ta ki yin aiki, gwamnatin Amurka  na iya sanya sabbin takunkumi kan daidaikun jami’an ICC.

Matsayin gwamnatin Trump na baya-bayan nan ya ginu ne kan takun saka a baya da hukumomin kasa da kasa. Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC da ke birnin Hague, ta fuskanci matsin lamba daga Washington tun bayan da ta bude bincike kan ayyukan sojan Amurka a lokacin yakin Afghanistan da kuma a baya-bayan nan, kan matakin da “Isra’ila” ta dauka a zirin Gaza.

Jami’an Trump sun bayyana irin wannan binciken a matsayin na siyasa da kuma cin zarafi ga ikon kasa, kamar dai yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5  December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi December 10, 2025 Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka
  • Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan: Reuters
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon