Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-15@08:24:37 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Published: 15th, April 2025 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana bakin cikinsa kan harin da aka kai  Jihar Filato wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40.

A cikin wata sanarwa, Shugaban kasa ya la’anci wannan tashin hankali tare da mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Caleb Mutfwang, Gwamnatin Jihar, da al’ummar Filato.

Sanarwar da Mai ba Shugaban Kasa shawara na musamman kan Harkokin Yada Labarai Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta bukaci Gwamnan da ya nuna cikakken ikonsa wajen warware rikicin da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin soyayya da hadin kai a maimakon  bambancin addini da kabila.

Ya bukaci shugabannin al’umma, da na addinai, da ma na siyasa a ciki da wajen jihar, da su hada kai domin kawo karshen ramuwar gayya da rikice-rikicen da suka jima suna addabar al’umma.

“Ya zaman wajibi a kawo karshen rikicin da ke faruwa tsakanin al’umma a Jihar Filato wanda ya samo asali daga rashin fahimta tsakanin kabilu da addinai daban-daban.” In ji Shugaba Tinubu.

“Na umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan wannan rikici, da gano wadanda ke da hannu a shirya wadannan ayyukan tashin hankali. Ba za mu amince da wannan barna da hare-haren ramuwar gayya ba. Ya isa haka.

Ya ce Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ba Gwamna Mutfwang da Gwamnatin Jihar Filato goyon baya wajen karfafa tattaunawa, inganta zaman tare, da tabbatar da adalci don magance wannan rikici har abada.

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Isra’ila ya kashe mutum 3 a kudancin Lebanon

Sojojin Isra’ila sun kashe akalla mutane uku a kudancin Lebanon a lokacin wasu hare-haren sama daban-daban bayan sun yi barazanar sake ci gaba da kai muggan hare-hare kan kasar.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta Lebanon ta fitar ta ce wani “harin makiya ” a yankin Yater, a kudancin kasar, ya kashe mutum daya tare da raunata wani.

A wani bangare kuma, wani harin Isra’ilar da aka kai kan wata mota shi ma ya kashe wani mutum a tsakanin garuruwan Safad al-Batikh da Barashit.

A lokaci guda kuma, an kashe wani memba na majalisar birnin Jouaya, Tyre, bayan wani hari da Isra’ila ta kai kan garin.

Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, a karshen watan da ya gabata, ya yi gargadin cewa Tel Aviv ta shirya kaddamar da sabon yaki kan Lebanon idan kungiyar Hezbollah ba ta mika makamanta ba kafin karshen shekarar nan ta 2025.

Lebanon ta samu sakon gargadin daga bangarorin kasashen Larabawa da na kasa da kasa cewa Isra’ila na shirin kaddamar da wani babban hari kan kasar, in ji Ministan Harkokin Waje Youssef Raggi a ranar Juma’a.

M. Raggi ya ce Beirut na kara karfafa huldarta da kasashen yankin don “kare Lebanon daga duk wani hari.”

Babban sakataren kungiyar Hezbollah, Sheikh Naim Qassem, a wani jawabi da ya yi kwanan nan, ya yi alkawarin cewa kungiyar ba za ta taba ajiye makamanta ba, yana mai sukar shirin gwamnatin kasar wanda y ace Amurka da Isra’ila ne ke amfani da batun don matsa lamba kan kungiyar ta kwance damarar makamai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Firaministan Ostiraliya ya goyi bayan tsauraran dokokin mallakar bindiga bayan harin Sydney December 15, 2025 Burtaniya: Masu Kin Baki Da Musulmi Suna Kai Masu Hare-Hare December 14, 2025 Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna December 14, 2025 Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia December 14, 2025 Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu December 14, 2025 Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bidiyon Turji ya yamutsa hazo tsakanin Matawalle da Gwamnatin Zamfara
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 3 a kudancin Lebanon
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai