Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-13@23:22:05 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Published: 15th, April 2025 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana bakin cikinsa kan harin da aka kai  Jihar Filato wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40.

A cikin wata sanarwa, Shugaban kasa ya la’anci wannan tashin hankali tare da mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Caleb Mutfwang, Gwamnatin Jihar, da al’ummar Filato.

Sanarwar da Mai ba Shugaban Kasa shawara na musamman kan Harkokin Yada Labarai Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta bukaci Gwamnan da ya nuna cikakken ikonsa wajen warware rikicin da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin soyayya da hadin kai a maimakon  bambancin addini da kabila.

Ya bukaci shugabannin al’umma, da na addinai, da ma na siyasa a ciki da wajen jihar, da su hada kai domin kawo karshen ramuwar gayya da rikice-rikicen da suka jima suna addabar al’umma.

“Ya zaman wajibi a kawo karshen rikicin da ke faruwa tsakanin al’umma a Jihar Filato wanda ya samo asali daga rashin fahimta tsakanin kabilu da addinai daban-daban.” In ji Shugaba Tinubu.

“Na umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan wannan rikici, da gano wadanda ke da hannu a shirya wadannan ayyukan tashin hankali. Ba za mu amince da wannan barna da hare-haren ramuwar gayya ba. Ya isa haka.

Ya ce Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ba Gwamna Mutfwang da Gwamnatin Jihar Filato goyon baya wajen karfafa tattaunawa, inganta zaman tare, da tabbatar da adalci don magance wannan rikici har abada.

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar Venezuela Nicholay Maduro ta wayar tarho inda ya bayyana masa cikakken goyonbaya bisa barazanar da kasar take fuskanta daga Amurka.

Fadar mulkin kasar ta Rasha ta ce, shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayi akan hanyoyin bunkasa alaka a tsakaninsu.

Tun a baya, a yayi wani zama da kwamitin tsaro na MDD ya yi, wakilan kasashen Venezuela, Rasha da China, sun yi tir da yadda Amurka take jibge sojiji a yankin Carriebia, tare da bayyana hakan a matsayin barazana ga zaman lafiyar duniya.

Kasashen uku sun kuma bayyana wajabci kare hurumin kasar Venezuela da kuma kaucewa tsoma baki a harkokin cikin gidanta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ben Gafir Ya Yi Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi AkanDoron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu   December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila