Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-11@13:11:23 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Published: 15th, April 2025 GMT

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana bakin cikinsa kan harin da aka kai  Jihar Filato wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40.

A cikin wata sanarwa, Shugaban kasa ya la’anci wannan tashin hankali tare da mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Caleb Mutfwang, Gwamnatin Jihar, da al’ummar Filato.

Sanarwar da Mai ba Shugaban Kasa shawara na musamman kan Harkokin Yada Labarai Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta bukaci Gwamnan da ya nuna cikakken ikonsa wajen warware rikicin da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin soyayya da hadin kai a maimakon  bambancin addini da kabila.

Ya bukaci shugabannin al’umma, da na addinai, da ma na siyasa a ciki da wajen jihar, da su hada kai domin kawo karshen ramuwar gayya da rikice-rikicen da suka jima suna addabar al’umma.

“Ya zaman wajibi a kawo karshen rikicin da ke faruwa tsakanin al’umma a Jihar Filato wanda ya samo asali daga rashin fahimta tsakanin kabilu da addinai daban-daban.” In ji Shugaba Tinubu.

“Na umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan wannan rikici, da gano wadanda ke da hannu a shirya wadannan ayyukan tashin hankali. Ba za mu amince da wannan barna da hare-haren ramuwar gayya ba. Ya isa haka.

Ya ce Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ba Gwamna Mutfwang da Gwamnatin Jihar Filato goyon baya wajen karfafa tattaunawa, inganta zaman tare, da tabbatar da adalci don magance wannan rikici har abada.

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Farfesa Amina Salihi Bayero, a matsayin sabuwar Shugabar Jami’ar Northwest.

Naɗin nata zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Disamban 2025, har zuwa tsawon shekaru biyar.

EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar, ta ce gwamnan ya amince da naɗin ne bayan  tantancewa da kwamitin gudanarwar jami’ar ya yi mata.

A matsayinsa na jagoran jami’ar, Gwamna Abba, ya yaba wa shugaban kwamitin da mambobinsa kan jajircewarsu wajen bin ƙa’idojin tantancewar.

Haka kuma ya nemi a yi mata addu’ar samun nasara wajen gudanar da jagorancin Jami’ar.

Farfesa Amina Salihi Bayero ƙwararriya ce a fannin Chemistry, musamman Analytical Chemistry, kuma ita ce mace ta farko da ta samu digiri na uku a fannin daga Jami’ar Bayero Kano.

Ta taɓa riƙe muƙamai da dama a harkar ilimi da gudanarwa, ciki har da shugabar sashen Chemistry, da kuma Mataimakiyar Shugabar Jami’a (DVC) a Jami’ar Yusuf Maitama Sule.

Ana girmama ta saboda jajircewarta wajen horar da matasan masana kimiyya.

Ana sa ran naɗin nata zai ƙara ɗaukaka martabar jami’ar, ya inganta tsarin ilimi, tare da bai wa mata ƙofar samun manyan muƙamai a Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda