Aminiya:
2025-09-17@21:53:39 GMT

Wani ɗan sanda ya harbe soja a Bauchi

Published: 28th, August 2025 GMT

Wani jami’in ’yan sandan kwantar da tarzoma (MOPOL) mai muƙamin Insfekta ya harbe wani soja har lahira a garin Futuk,  da ke Ƙaramar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.

Aminiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne bayan wata taƙaddama da ta taso kan wata mota mai ɗauke da ma’adinai da ake zargin ta wani kamfanin haƙar ma’adinai na ƙasar Sin ce.

ASUU: Malaman Jami’ar FUK sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura  A ɗora min laifin hatsarin jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja — Shugaban NRC

Mai riƙon muƙamin Daraktan Hulɗa da Jama’a na rundunar soji, Laftanar Solomon Atang Hallet, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kama ɗan sandan da ake zargi, kuma ana ci gaba da bincike tsakanin rundunar soji da ta ’yan sanda.

Shaidun gani da ido sun ce, lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, jim kaɗan bayan sallar Magrib, lokacin da sojoji suka dakatar da wata mota da ke ɗauke da ma’adinai daga wurin haƙar Yalo.

Sai dai direban motar ya biris da dakatarwa ya ƙi tsayawa a shingen da sojojin suka kafa, lamarin da ya sa aka biyo shi har cikin garin Futuk.

A nan ne aka samu hatsaniya tsakanin sojojin da ɗan sandan da ake zargin shi ne yake rakiya motar.

Bayanai sun ce a lokacin da cacar baki ta ɓarke, sai ɗan sandan ya ɗauki bindiga ya harbi shugaban tawagar sojojin a baya, inda aka yi nasarar cafke shi tare da karɓe bindigar, yayin da direban motar ya tsere.

Wata majiya ta tabbatar da cewa motar na ɗauke da ma’adinai masu daraja da ake zargin an haƙo su ba bisa ƙa’ida ba, tare da zargin cewa ɗan sandan na rakiya ne a wajen aikin.

An garzaya da sojan da aka harba zuwa asibiti a Gombe, amma daga baya ya rasu sakamakon raunukan da ya samu.

Mazauna yankin Futuk sun ce ƙarar bindigar ta firgita jama’a, inda mazauna da ’yan kasuwa suka rufe shaguna suka gudu gida saboda fargabar tashin hankali.

Wani babban jami’i a Alkaleri ya yaba wa sojojin da suka kai zuciya nesa ba tare da sun ɗauki doka a hannunsu ba, sai dai sun tabbatar da kama ɗan sandan da motar.

Duk ƙoƙarin da wakilinmu ya yi don jin ta bakin Kakakin ’yan sandan Bauchi, SP Ahmed Wakil, ya cia, domin bai ɗaga kira ko amsa saƙonni ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Wasu mazauna yankin sun yi kira ga hukumomin tsaro da su binciki zargin shiga jami’an tsaro cikin harkar haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, suna mai cewa lamarin na iya zama barazana ga tsaro da zaman lafiya a jihar.

A halin yanzu, kwamishinan ’yan sandan jihar ya ziyarci kwamandan rundunar soji a Bauchi, Birgediya-Janar U.J. Simon, domin kwantar da hankali da tabbatar an gudanar da sahihin bincike.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi ɗan sandan

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

 

Danja ya ce, sojojin a yayin da suke aiki da sahihan bayanan sirri dangane da shirin kai hari kan al’ummar Chanchangi da kungiyar ta’adda ta Bojo ke shirin yi a ranar 15 ga Satumba, 2025, sun yi artabu da ‘yan ta’addan a kan hanyar Demeva zuwa Chanchangi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa