Leadership News Hausa:
2025-10-15@22:16:23 GMT

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Published: 11th, April 2025 GMT

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, bisa gayyatarsa da sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Vietnam kuma shugaban jamhuriyar gurguzu ta Vietnam ya yi, shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai kai ziyarar aiki kasar daga ranar 14 zuwa 15 ga wata.

 

Haka kuma, bisa gayyatarsa da firaministan kasar Malaysia da sarkin Cambodia suka yi, shugaban na kasar Sin kuma sakatare janar na JKS, zai ziyarci kasashen Malaysia da Cambodia daga ranar 15 zuwa 18 ga wata.

(Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike

Kotun Babban Majistare da ke Yaba ta bayar da umarnin a tono gawarwakin mutane 10 da gobara ta kashe a ginin Afriland Towers da ke Legas a ranar 16 ga Satumba, 2025, domin a gudanar da bincike a kansu.

Alkalin kotun, Mai shari’a Atinuke Adetunji ce ta bayar da umarnin a ranar Talata bayan ta samu labarin cewa an riga da binne wasu daga cikin waɗanda gobarar ta ritsa da su.

“Mai ƙorafi ya rubuta wa Gwamnatin Jihar Legas don neman izinin tono gawarwakin waɗanda suka mutu, sannan a gudanar da bincike a kansu,” in ji Mai Shari’a Adetunji.

Wannan umarni ya biyo bayan wata wasiƙa daga ofishin babban lauya Femi Falana da aka aike wa Babban Mai Kula da Gawarwaki na Jihar Legas, Mai Shari’a Mojisola Dada, a ranar 29 ga watan Satumba, 2025.

Femi Falana (SAN), ta hannun ofishinsa, ya shigar da ƙorafi ga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Legas, yana neman a gudanar da binciken gawarwaki don gano musabbabin mutuwar da kuma tabbatar da adalci.

A zaman farko na shari’ar, Mai Shari’a Adetunji ta umurci dukkan ɓangarorin da suka halarta da su gabatar da takardun da suka dace kafin zaman kotun na gaba.

Kotun ta kuma gayyaci hukumomi da kamfanoni da suka haɗa da bankin UBA da Hukumar Tara Haraji ta Tarayya (FIRS), Ma’aikatar Kashe Gobara, Afriland Towers, United Capital, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA), Hukumar Tsaro ta Jihar Legas, da sauran masu ruwa da tsaki.

Adetunji ta ƙara da umartar mai ƙorafi da ya tuntubi iyalan waɗanda suka mutu don gano waɗanda ke da niyyar a tono gawar ’yan uwansu domin a gudanar da binciken gawarwaki.

Ta kuma nemi shaidun gani da ido da su bayyana don bayar da bayani kan abin da ya faru.

Lauya Yahaya Atata daga ofishin Falana ya shaida wa kotu cewa zaman na ranar an shirya shi ne don haɗa dukkan masu ruwa da tsaki da kuma fayyace yadda za a gudanar da binciken gawarwaki.

Sai dai alkalin ta lura cewa lauyoyin ba su shirya sosai ba, kuma ta jaddada cewa binciken ba zai ci gaba ba sai an gabatar da dukkan takardun da ake bukata.

Wani lauya mai wakiltar ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu, A. O. Mema, ya shaida wa kotu cewa abokinsa, Peter Ifaranmaye, wanda shi ne manaja a Hukumar Tara Haraji ta Tarayya, an riga da binne shi.

Bayan wannan bayani, alkali Adetunji ta jaddada cewa yin binciken gawarwaki yana da matuƙar muhimmanci.

“Binciken gawarwaki muhimmin abu ne. Ba za mu iya gudanar da bincike ba sai an yi bincike don a gano hakikanin abin da ya faru,” in ji ta.

Kotun ta dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Nuwamba, 2025.

Gobarar ta tashi ne a ginin Afriland Towers, wani katafaren ginin kasuwanci da ke titin Broad a unguwar Legas Island, a ranar 16 ga watan Satumba, inda ta kashe akalla mutane 10 tare da jikkata wasu da dama.

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da sassafe, kuma ta bazu cikin ginin da sauri kafin hukumomin kasha gobara su samu damar shawo kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia
  • Majalisar Dattawa za ta tantance Amupitan a ranar Alhamis
  • Matakin Da Kasashen Yamma Su Ka yi Na Maidowa Da Iran Takunkumi Ya Sabawa Doka.
  • Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Dirar Mikiya Kan Donald Trump Kan Bai Wa Isra’ila Makamai
  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani