Leadership News Hausa:
2025-11-14@21:01:50 GMT

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Published: 11th, April 2025 GMT

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, bisa gayyatarsa da sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Vietnam kuma shugaban jamhuriyar gurguzu ta Vietnam ya yi, shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai kai ziyarar aiki kasar daga ranar 14 zuwa 15 ga wata.

 

Haka kuma, bisa gayyatarsa da firaministan kasar Malaysia da sarkin Cambodia suka yi, shugaban na kasar Sin kuma sakatare janar na JKS, zai ziyarci kasashen Malaysia da Cambodia daga ranar 15 zuwa 18 ga wata.

(Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Ya Yi Kira Ga Jama’a Su Yi Rijista Kuma Su Karɓi Katin Zaɓe

Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa da ke Jihar Kano, Yusuf Shuaibu Imam, ya yi kira ga mazauna yankin da su ziyarci ofisoshin Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) domin yin rijistar zaɓe da kuma karɓar Katin Zaɓe na Dindindin (PVC).

Imam ya yi wannan kiran ne yayin da yake kaddamar da jerin ayyukan raya al’umma a mazabar Tudun Wada da Gama.

Ya jaddada muhimmancin matasa, musamman waɗanda suka kai shekaru 18 a kwanan nan, da kuma waɗanda suka rasa ko katinsu ya lalace, da su tabbatar sun yi rijista domin su samu damar shiga cikin zaɓuɓɓukan da za su zo nan gaba.

Shugaban karamar hukumar ya ce yin rijistar zaɓe hanya ce ta bai wa ‘yan ƙasa damar cika haƙƙin su na dimokuraɗiyya da kuma zaɓar shugabanni na gari masu cancanta da gaskiya.

A wani bangare na jawabin nasa, Imam ya sake nanata kudirin gwamnatinsa na haɓaka ci gaban, inda ya kaddamar da ayyuka sabbi guda bakwai, wanda suka haɗa da gine-ginen magudanan ruwa da gadaje da akwaku a wasu yankuna na Tudun Wada da Gama.

Khadijah Aliyu/Kano

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand
  • Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
  • Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
  • Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
  • Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Ya Yi Kira Ga Jama’a Su Yi Rijista Kuma Su Karɓi Katin Zaɓe
  • Wata Gidauniya Ta Kaddamar Da Kwamiti Kan Mata A Nasarawa
  • Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
  • An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa
  • Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
  • Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa