Na Dauki Karramawar Jaridar LEADERSHIP Da Matukar Muhimmanci – Gwamna Abba
Published: 11th, April 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Karramawa Lambar Yabo
এছাড়াও পড়ুন:
Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia
Gwamnan Jihar Binuwai, Hyacinth Alia, ya ce babu wani addini ko mabiyansa da ake yi wa kisan ƙare dangi a jiharsa ko a Najeriya baki ɗaya.
Ya yi wannan jawabi ne a ranar Laraba a wani taron da Hukumar Kare Haƙƙin Dan Adam ta Ƙasa (NHRC) ta shirya a Abuja kan kare haƙƙoƙin mutanen da aka tilasta musu barin gidajensu.
Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A CikiGwamna Alia, wanda tsohon Faston Katolika ne, ya ce: “A Binuwai, babu wani kisan kare addini, ƙabilanci, launin fata, ƙasa ko jiha.
“Muna da wasu matsalolin tsaro, amma ba kisan addini ba ne. Ya kamata mutane su duba ma’anar kisan ƙare addini ta Majalisar Ɗinkin Duniya.”
Ya kuma ce babu wani jihadi da ake yi a kowane ɓangare na Najeriya, ko da yake ƙungiyoyin ’yan ta’adda kamar Boko Haram da ISWAP a Arewa Maso Gabas, suna iƙirarin jihadi.
“Babu wani jihadi a Najeriya,” in ji Alia.
“A matsayina na Fasto kuma gwamna, ni ne zan fara yin magana idan hakan na faruwa a jihata ko a wani ɓangare na ƙasar nan.”
Kalamansa na zuwa ne a daidai lokacin da Amurka ke zargin ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya.
Amurka ta taɓa sanya Najeriya a cikin jerin “Ƙasashen Masu Matsala ta Musamman” saboda cin zarafin addini, amma gwamnatin Najeriya ta musanta wannan zargi.
Kiristoci da Musulmai duka sun sha wahala sakamakon rashin tsaro, fashi da makami, da kuma garkuwa da mutane.
Gwamna Alia, ya ce ya gana da ofishin jakadancin Amurka don bayyana yadda halin tsaro yake a Binuwai.
“Na bayyana cewa babu kisan ƙare addini a Najeriya, musamman a Binuwai. Ma’anar Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta dace da yanayin nan ba,” in ji shi.
Jihar Binuwai ta jima tana fuskantar matsalolin da suka shafi kisan jama’a da sace mutane.
Bayanai sun nuna cewa sama da mutum 800 sun mutu, yayin da aka sace kusan mutum 400 cikin shekaru biyu da suka gabata.
A watan Yuni, aƙalla mutum 100 ne suka mutu a hare-haren da ’yan ta’adda suka kai a Ƙaramar Hukumar Guma.