Wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ba da fifiko wajen dakatar da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi wa kasar Labanon.

A cewar Al-Mayadeen Hassan Fadlallah mamba a bangaren Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya ce: Dakatar da wuce gona da iri kan kasar Labanon wani muhimmin al’amari ne na kasa da ya zama wajibi a sanya shi cikin ajandar gwamnatin Lebanon.

Ya kara da cewa: Al’ummar kasar Labanon suna fuskantar wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawan tare da yin kira ga gwamnati da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na dakile wannan ta’addanci.

Fadlallah dai ya dauki babbar matsalar kasar Labanon a matsayin mamaya da kuma keta hurumin kasar, yana mai jaddada cewa wasu na son jefa kasar cikin rudani da ruguza karfin da kasar ta Lebanon ke da shi na tunkarar mulkin kama-karya na kasashen waje. Irin wadannan ayyuka sun saba wa muradun kasar Lebanon, kuma sun yi daidai da muradin makiya.

Hassan Fadlallah ya musanta ikirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa Hizbullah na amfani da tashar jiragen ruwa na Beirut wajen safarar makamai, ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar Lebanon da su dauki mataki kan masu yada wadannan karairayi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Labanon

এছাড়াও পড়ুন:

Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada cewar Muhammadu Sanusi II ne, halastaccen Sarki a hukumance 

Ya bayyana haka ne a ranar Asabar, a lokacin bikin yaye ɗalibai karo na huɗu a Jami’ar Skyline University of Nigeria (SUN) da ke Kano.

Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94

“Muhammadu Sanusi II shi kaɗai ne Sarkin Kano a wajen mutane da gwamnatin jiha. Duk wani da aka naɗa daga wajen jihar ba shi da inganci a idon al’ummar Kano.”

A cewarsa, duk wanda wasu suka naɗa a matsayin Sarki ba shi da ƙima a idon al’ummar Kano da gwamnatin jihar.

Kwankwaso, wanda ya yi takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP a 2023, ya yaba wa jami’ar saboda samar da ingantaccen ilimi.

Ya shawarci matasa su dage wajen neman ilimi domin nan na gaba za su iya jagorantar ƙasar.

Yayin da yake magana kan rikicin masarauta a Kano, Kwankwaso ya jaddada cewa Muhammadu Sanusi II ne, Sarki halastacce.

Kwankwaso ya nuna damuwa kan hare-haren ’yan bindiga a Kano

Haka kuma ya nuna damuwa game da ƙaruwa hare-haren ’yan bindiga daga Jihar Katsina da ke kai wa yankunan Tsanyawa, Shanono, Gwarzo da Karaye hare-hare.

Ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ɗaukar mataki domin magance barazanar.

Ya ce idan gwamnati ba za ta iya kare rayuka da dukiyoyi ba, to lallai sai ta sake nazari kan yadda ta ke jagoranci.

Ya ƙara da cewa matsalar tsaro da ta samo asali a Zamfara ta bazu zuwa Sakkwato, Kebbi, Kaduna, sannan yanzu tana barazanar tsallakowa zuwa Kano da Jigawa.

“Idan gwamnati ba za ta iya kare rayuka da dukiyoyi ’yan ƙasa ba, to lallai dole ta zauna ta sake tunani. Matsalar tsaro da ta fara a Zamfara ta bazu zuwa Sakkwato, Kebbi, Kaduna, sannan yanzu tana barazana ga Kano da Jigawa.”

Kwankwaso, ya nuna yadda ya kashe maƙudan kuɗaɗe don samar da tsaro a lokacin da ya yi gwamna, sannan ya roƙi gwamnati mai ci ta shugaba Bola Ahmed Tinubu da ta ƙara himma wajen kare ’yan Najeriya.

A nasa ɓangaren, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, wanda shi ne jagoran Jami’ar, ya shawarci waɗanda suka kammala karatu da su zama masu gaskiya.

Ya ce ilimi ba shi da amfani idan ba a yi amfani da shi wajen kawo canji ba.

Ya nuna farin cikinsa kan samun mata da suka kammala karatu, inda ya yi fatan samun mata a harkokin shugabanci.

Tun da farko, Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Ajith Kumar V.V., ya bayyana cewa ɗalibai 24 daga cikin 180 sun samu sakamako mafi daraja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
  • Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya
  • Lebanon za ta shigar da kara a kan Isra’ila a MDD game da gina Katanga a iyakarta
  • Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso
  • Kasashen Latin Amurka Sun Shirya Tsaf Don Mayar Da Martani Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Kan Venuzuwela
  • EU ta bukaci Isra’ila ta dauki mataki don kawo karshen tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan
  •  Unrwa: Fiye Da Gidaje 282,000 “Isra’ila” Ta Rusa A Gaza
  • Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya