Wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ba da fifiko wajen dakatar da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi wa kasar Labanon.

A cewar Al-Mayadeen Hassan Fadlallah mamba a bangaren Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya ce: Dakatar da wuce gona da iri kan kasar Labanon wani muhimmin al’amari ne na kasa da ya zama wajibi a sanya shi cikin ajandar gwamnatin Lebanon.

Ya kara da cewa: Al’ummar kasar Labanon suna fuskantar wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawan tare da yin kira ga gwamnati da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na dakile wannan ta’addanci.

Fadlallah dai ya dauki babbar matsalar kasar Labanon a matsayin mamaya da kuma keta hurumin kasar, yana mai jaddada cewa wasu na son jefa kasar cikin rudani da ruguza karfin da kasar ta Lebanon ke da shi na tunkarar mulkin kama-karya na kasashen waje. Irin wadannan ayyuka sun saba wa muradun kasar Lebanon, kuma sun yi daidai da muradin makiya.

Hassan Fadlallah ya musanta ikirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa Hizbullah na amfani da tashar jiragen ruwa na Beirut wajen safarar makamai, ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar Lebanon da su dauki mataki kan masu yada wadannan karairayi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Labanon

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran

Babban hafasan hafsoshin kasar Iran Major General Abdolrahim Mousavi ya bayyana cewa idan HKI ta kuskura ta sabonta yaki da kasar Iran ta zata fuskanci maida martani mafi tsanani.

Janar Musawi ya bayyana haka ne a jiya laraba a lokacinda yake hira da tashar talabijan ta almayaden ta kasar Lebanon

Ya kuma kara da cewa a yakin da ya gabata wato wa’adussadik na ukku na watan da ya gabata, sojojin Iran basu fitar da dukkan makamansu su. Ko kuma dukkan karfinsu ba. Don haka idan yahudawan sun  kukura sun sake farfado da yaki da JMI sai sun hadu da martani wanda ya fi na farko zafi,

Janar Musavi ya kara da cewa HKI ta dauki shekaru tana tanajin ranar da yaki zai hadata da JMI, kuma ta ga inda tanadinta yak are. Ya ce abinda yake gaba gareta ya fi muni idan bata sani ba ta sani.

A wabi bangare Janar Musawi ya bayyana cewa kasashen yamma da kuma HKI sun son amfani da shirin makamashin nukliya na kasar Iran don raba kasar Iran da kuma maida ita fiye da yadda take a zamanin nsarki sha. Amma tare da taimakon All..sun kasa yin haka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran
  •  Sheikh Na’im Kassim:  Ba Za Mu Taba Mika Makamanmu Ga Makiya Ba