Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
Published: 11th, April 2025 GMT
Wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ba da fifiko wajen dakatar da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi wa kasar Labanon.
A cewar Al-Mayadeen Hassan Fadlallah mamba a bangaren Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya ce: Dakatar da wuce gona da iri kan kasar Labanon wani muhimmin al’amari ne na kasa da ya zama wajibi a sanya shi cikin ajandar gwamnatin Lebanon.
Ya kara da cewa: Al’ummar kasar Labanon suna fuskantar wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawan tare da yin kira ga gwamnati da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na dakile wannan ta’addanci.
Fadlallah dai ya dauki babbar matsalar kasar Labanon a matsayin mamaya da kuma keta hurumin kasar, yana mai jaddada cewa wasu na son jefa kasar cikin rudani da ruguza karfin da kasar ta Lebanon ke da shi na tunkarar mulkin kama-karya na kasashen waje. Irin wadannan ayyuka sun saba wa muradun kasar Lebanon, kuma sun yi daidai da muradin makiya.
Hassan Fadlallah ya musanta ikirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa Hizbullah na amfani da tashar jiragen ruwa na Beirut wajen safarar makamai, ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar Lebanon da su dauki mataki kan masu yada wadannan karairayi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Labanon
এছাড়াও পড়ুন:
An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
Gwamnatin Jihar Bauchi ta ba da umarnin rufe dukkan makarantun firamare, sakandare, da manyan makarantu—ciki har da makarantun Gwamnatin Tarayya da makarantu masu zaman kansu saboda matsalolin rashin tsaro da ke faruwa a faɗin ƙasar kan.
Sanarwa da Jalaludeen Usman Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi, ya fitar ta ce, “Wannan shawara, duk da cewa tana da wahala, Gwamnatin Jihar Bauchi ta yanke ta ne bayan tattaunawa mai zurfi da kuma la’akari da matsalolin tsaro da suka shafi tsaron ɗalibai, malamai, da al’ummomin makarantu a faɗin jihar.”
“Gwamnati ta san abin da wannan matsala ka iya haifarwa. Duk da haka, kare ’ya’yanmu ya kasance babban nauyin da ke kanmu. Muna sane da cewa lowane ɗalibi a Jihar Bauchi ya cancanci ya yi karatu a cikin yanayi mai aminci, kwanciyar hankali, kuma ba tare da tsoro ba.
“Saboda haka muna kira ga iyaye, masu kula, masu mallakar makarantu, da duk masu ruwa da tsaki da abin ya shafa da kada su firgita, amma su kwantar da hankalinsu su kuma ba da haɗin kai.”
“Gwamnati tana aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro don magance matsalolin cikin sauri da kuma cikakkiyar fahimta, tare da tabbatar da cewa ayyukan ilimi na yau da kullum, za su ci gaba da gudana da zarar an tabbatar da hakan.
“Muna kuma kira ga jama’a da su ci gaba da taka tsantsan. Idan kun ga wani abu da ba ku gane ba ku bayar da bayani wa jami’an tsaro saboda bayar da bayanai da a kan lokaci suna da mahimmanci wajen kare al’ummominmu.
“Gwamnatin Jihar Bauchi za ta ci gaba da samar da sabbin bayanai yayin da lamarin ke ci gaba.”