Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku ya kasance mai fafutukar tabbatar da hadin kan ‘yan adawa, yana mai jaddada muhimmancin hadin gwiwa wajen kayar da Tinubu a zaben 2027.

A ranar 8 ga watan Maris ne ya bayyana kokarinsa na hada kan ‘yan adawa da kafa kawancen korar jam’iyyar APC.

Bayan sauya shekar El-Rufa’i daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PSP a ranar 10 ga watan Maris, tattaunawar da aka yi tsakanin shugabannin ‘yan adawa ta samu gagarumar nasara.

Atiku da sauran ‘yan adawa sun bayyana cewa taron na ranar 20 ga watan Maris ya nuna kaddamar da kawancen a hukumance.

A baya dai an ruwaito a ranar 23 ga watan Maris cewa ana jinkirin tattaunawa kawance tsakanin shugabannin siyasa saboda burin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku na tsayawa takara da kuma rikicin shiyya.

Majiya ta bayyana cewa masu ruwa da tsaki suna da zabi da yawa don magance duk abubuwan da lamarin ya kunsa.

Majiyar ta ce, “Akwai batutuwa da dama a tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki a tattaunawar kawancen, inda batun arewa da kudu shi ne babban abin da ya fi daukar hankali.

“Yawancinmu mun fahimci cewa idan muka tsayar da dan takarar kudu wanda ya cancanta kuma mai gaskiya, kayar da Shugaba Tinubu zai fi sauki. Don haka da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki, musamman na arewa, suna kira ga Atiku a kan kar ya tsaya takara, ya bai wa kawancen damar mara wa dan takarar kudancin kasar nan baya da zai yi wa’adi daya idan aka zabe shi.

“A hakika, wasu daga cikin wadannan masu ruwa da tsaki sun dagewa cewa duk wani dan takara daga kudu da za su mara masa baya dole ne ya amince da alkawarin wa’adi daya.

“Wadannan al’amura sun kunno kai, amma mun himmatu wajen magance su a lokacin da suka taso da kuma daukar nauyin ‘yan Nijeriya da dama da suke fuskantar rashin iya shugabancin APC. Manufarmu ita ce tabbatar da ingantaccen tsari wanda ke wakiltar muradun jama’a da karfafa hadin kan kawancen.”

A lokacin da aka yi yunkurin jin ta bakinsa, sakataren kungiyar hadin kan jam’iyyun siyasa ta kasa, Peter Ahmeh, ya tabbatar da cewa masu ruwa da tsaki na yin la’akari da shawarar fitar da dan takara daga kudancin kasar nan tare rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi guda.

Ahmeh ya bayyana cewa, kawancen ‘yan adawar da ke adawa da Shugaba Tinubu sun fi wadanda tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan ya fuskanta a shekarar 2014.

Ya ce, “Rattaba hannu kan yarjejeniyar wa’adi guda da dan takara daga kudu na daga cikin abin da ke kan teburin tattauwar, amma har yanzu ba a kammala hakan ba. Bai kai ga karshe ba.

“Peter Obi da wasu masu neman takar shugaban kasa a kudu suka cikin wannan tattaunawa. Na yi imanin cewa za a cimma matsaya nan da ‘yan makonni masu zuwa.

“Akwai zabi masu yawa a kan tebur. Mutane suna kawo sauye-sauye daban-daban, amma gaskiya har yanzu ba a cimma matsaya ba. Da zaran an cimma matsaya kan wannan yarjejeniyar, za mu sanar da al’umma.

“A bayyane yake cewa ‘yan Nijeriya da yawa sun fahimci cewa wannan gwamnati tana cutar da mu fiye da alherinta. Don haka, ‘yan Nijeriya da dama ne ke shiga kawancen. Akwai ‘yan adawa da ke adawa da wannan gwamnati fiye da yadda ake yi wa tsohon shugaban kasar Jonathan a shekarar 2014.

“Don haka, ina kira ga dukkan masu ruwa da tsaki na kkwancen da sauran shugabannin ‘yan adawa da su ci gaba da wannan alkawari domin mu hada kai don ceto kasar nan daga gazawar APC.”

Lokacin da aka tuntubi tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku kai ji ta bakinsa kan wannan kawance, ya yi gargadi game da rade-radin da ka iya kawo cikas ga tattaunawar kawancen.

Atiku, ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya jaddada cewa duk wata yarjejeniya da aka kulla za ta kasance wajibi ga dukkan bangarorin da abin ya shafa.

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntubar juna a fadin kasar nan kan wannan kawancen ‘yan adawa.

Sai dai kuma shugaban matasan jam’iyyar PDP, Timothy Osadolor, ya soki yunkurin da ake yi na dan kudu ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi daya, yana mai cewa lamarin ba mai yiwuwa ba ne.

Da yake mayar da martani kan kawancen ‘yan adawa, Daraktan Yada Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya yi watsi da yunkurin kawancen, inda ya bayyana cewa farin jinin jam’iyya mai mulki a tsakanin ‘yan Nijeriya na karuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kawance masu ruwa da tsaki ga watan Maris yan Nijeriya bayyana cewa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Sauran sun haɗa da: Hon. Ibrahim Adamu Sarki a jam’iyyar PDP daga shiyya ta biyu sai , Nazifi Jibrin Muhammad na jam’iyyar PDP daga shiyya ta biyu da Haruna Dogo Mabo na.jamiyya NNPP daga shiyya biyu sai Honorable Isah Dan Maryam na PRP daga shiyya ta biyu da , Honarabul Isaac Auta Zankai na jam’iyyar SDP da Wilson Iliya Yange na jam’iyyar PDP, da Honarabul Simon Na Allah na jam’iyyar LP, sai Ibrahim Musa na jam’iyyar ADC daga shiyya ta biyu shi ne Sakataren kwamitin.

 

Da yake jawabi bayan kaddamar da kwamitin, Shugaban jam’iyyar na jihar, Elder Patrick Ambut, ya shawarci mambobin da su kasance masu jajircewa tare da tabbatar da adalci da gaskiya a cikin aikin da aka dora musu.

 

“Kalubalen aikin yana da girma kuma yana buƙatar jajircewa, adalci, da gaskiya,” in ji shugaban jam’iyyar”

 

Daga cikin ayyukan da aka ɗora wa kwamitin har da: yin binciken shugabanci a dukkan ƙananan hukumomi 23 da mazabu, tare da daidaita tsarin jam’iyyar da baban taron jam’iyyar na 2022 da hukumar INEC ta kula da shi.

 

A cikin jawabinsa na karɓar nauyin shugabanci, Shugaban Kwamitin, Philimon Kure, ya bayyana cewa ayyukan da aka ɗora musu sun bayyana sosai, yana mai cewa gudunmawar kowa da kowa ce za ta tabbatar da gina jam’iyya mai ƙarfi wacce za ta kare muradun dukkan mambobi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu  November 12, 2025 Labarai ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi November 12, 2025 Manyan Labarai Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
  • Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
  • Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa