Leadership News Hausa:
2025-10-18@10:01:48 GMT

Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo

Published: 11th, April 2025 GMT

Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo

A ƙalla shaguna 12 sun ƙone ƙurmus sakamakon gobarar da ta tashi da daddare a Agodi Gate, birnin Ibadan, babban birnin Jihar Oyo. Lamarin ya faru ne a daren Alhamis a ginin Block A  na kasuwar Siminti ta Mayegun, Araromi, kamar yadda hukumar kashe gobara ta Jihar Oyo ta tabbatar.

Shugaban hukumar, Akinyemi Akinyinka, ya bayyana cewa jami’ansu sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 11:02 na dare, inda nan take suka tura tawaga ƙarƙashin jagorancin Cfs Jimoh.

Bayan isarsu, sun tarar da shaguna da dama na ci da wuta, amma cikin gaggawa suka dakile yaɗuwar gobarar zuwa sauran shagunan da ke kusa.

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri Gobara Ta Ƙone Sabon Ginin Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Mata Na Jami’ar Sokoto 

Akinyinka ya bayyana cewa gobarar ta samo asali ne daga wutar lantarki mai ƙarfi. Ya ƙara da cewa an kare dukiyoyi da darajarsu ta kai biliyoyin Naira a kasuwar, duk da cewa shaguna 12  sun ƙone baki ɗaya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

Sabbin alkaluman da babbar hukumar kula da haraji ta kasar Sin ta bayar yau 17 ga wata sun nuna cewa, a cikin watannin tara na farkon bana, kamfanoni sun kara zuba jari wajen kirkire-kirkire, kuma sabbin masana’antu bisa manyan tsare-tsare sun ci gaba da habaka. Lamarin da ya shaida cewa, ana samun ci gaba cikin sauri wajen raya sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi mai dorewa ta kasar Sin.

 

Zhang Bin, darektan kwamitin jam’iyyar kwaminis ta Sin dake cibiyar nazarin dabarun tattalin arziki da hada hadar kudi ta kwalejin kimiyyar zamantakewar al’umma ta kasar Sin,ya bayyana cewa, bisa alkaluman da hukumar harajin ta fitar, ana iya ganin cewa, ana kara habaka sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi mai dorewa a kasar Sin, lamarin da zai taimaka sosai wajen bunkasuwar ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar.(Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki October 17, 2025 Daga Birnin Sin Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth October 17, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Kauyuka Guda Uku Na Kasar Sun Shiga Cikin Kauyukan Yawon Shakatawa Ta Duniya
  • An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
  • 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a
  • Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike