Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon
Published: 17th, March 2025 GMT
A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon ta yankin Hermul
Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.
Kungiyar ta Tahrirush-sham ta yi amfani da makamai rokoki da atalare wajen kai hari daga kan iyaka.
Tuni dai kungiyar Hizbullah ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta karyata zargin na kungiyar Tahrirus-sham.
Ofishin da yake kula da watsa labaru na Hizbullah ya bayyana cewa; Babu gaskiya a cikin labaran da ake watsawa na cewa Hizbullah tana da hannu a cikin abinda yake faruwa akan iyakar Lebanon da Syria.”
Sanarwar ta kuma kara da cewa; Muna sake jaddada cewa ba mu da alaka da duk wani abu da yake faruwa a cikin kasar Syria.
Wata kafa ta watsa labarai ta kasar Lebanon ta ce; kungiyar Agaji ta “Red Cross” ta mika gawawwakin wasu mayakan kasar Syria su uku da aka kashe, ba tare da cikakken bayanin yadda aka kashe sub a.
Haka nan kuma majiyar ta bayyana cewa; an harba makamai masu linzami a cikin garin al-kasar da yake akan iyaka.
Ma’aikatar tsaron Syria ta sanar da kai hari da manyan bindigogi akan wasu garuruwa Lebanon da suke a kan iyaka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Manjo Janar Hussain Salami ya fada a yau Alhamis cewa; Abokan gaba suna yi mana barazana da yaki, sannan ya tabbatar da cewa a shirye suke su fuskanci duk abinda zai faru.
Manjo janar Salami wanda ya gabatar da jawabi ga taron dakarun sa-kai na “Basiji a nan Tehran ya kuma kara da cewa; Babu wani wuri komai zurfi da nisansa a HKI da ba mu tsinkayowa, idan kuwa aka ba mu umarni to za su yi nasara, mu Sanya abokin gaba ya yi nadama.
A gefe daya ministan tsaron Iran ya bayyana cewa; Duk wani hari da ake tunanin kawo wa Iran, to kuwa zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Ministan tsaron na Iran Laftanar janar Azizi Nasri Zadeh ya kara da cewa; Idan har yaki ya barke, to za a tilasta wa Amruka ficewa daga wannan yankin, kuma asarar da za ta yi sai ta rubanya wacce za ta yi wa Iran.”
Ministan tsaron na Iran ya kuma ce; Abin takaici ne yadda wasu jami’an Amurka su ka yi barazanar yiyuwar barkewar yaki, idan ba a cimma matsaya ba a tattaunawar Nukiliya, sannan ya kara da cewa: Tehran ba ta maraba da yaki, amma kuma a lokaci daya ta shirya masa.”