Saboda Rikicin Kasar Sudan Ta Kudu Shugaba Musaveni Ya Isa Birnin Juba
Published: 4th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni ya isa birnin Juba na kasar Sudan ta kudu a yau Juma’a, a kokarin lalubo hanyar warware dambaruwar siyasar da kasar take ciki da hana barkewar sabon yakin basasa.
Jim kadan bayan yi wa mataimakin shugaban kasar Riek Machar daurin talala a gidansa ne kasar ta shiga zaman dar-dar da fargabar sake komawa cikin yakin basasa.
Da akwai kawance a tsakanin shugabannin kasashen Uganda Mosaveni da kuma Silva Kiir na kasar Sudan Ta Kudu. Kwanaki kadan da su ka gabata ne dai kasar ta Uganda ta aike da sojoji masu yawa zuwa kasar ta Sudan ta Kudu, domin bayar da kariya ga gwamnatin Juba.
Gwamnatin Salva Kir tana zargin Machar da cewa yana rura wutar wani sabon yaki a cikin kasar. A ranar Laraba ta makon da ya shude ne dai aka yi wa mataimakin shugaban kasar daurin talala a gidansa saboda fadan da ake yi a yankin Upper Nile tsakanin sojojin gwamnati da kuma masu dauke da makamai na rundunar “White Army”.
Tawagar tarayyar Afirkan da ta isa birnin Juba wacce ta kunshi majalisar dattijan nahiyar Afirka, a kokarin shawo kan rikicin da kasar ta fada.
Tarayyar Afirkan ta fara kokarin shiga tsakani ne, bayan daurin talala da aka yi wa mataimakin shugaban kasa Riek Machar a gidansa,lamarin da ya sake jefa kasar cikin zaman dar-dar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan na zargin Janar Haftar na Libiya da goyon bayan hare-haren ‘yan tawayen kasarta
Sojojin Sudan da ma’aikatar harkokin wajen Sudan sun zargi Janar Khalifa Haftar mai ritaya da goyon bayan hare-haren da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kaddamar a kan iyakokin Sudan da Masar da Libya.
A cewar sanarwar da Rundunar Sojin Sudan ta fitar, Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Rapid Support Forces da ke samun goyon bayan Bataliyar Salafiyya ta Haftar, sun kai hare-hare kan iyakokin Sudan da Masar da Libya, da nufin kwace wadannan yankuna masu matukar muhimmanci.
Sanarwar ta kara da cewa: Wannan shiga tsakani da dakarun Haftar suka yi kai tsaye ya zama “cin zarafi a fili” ga ‘yancin Sudan da al’ummarta, tare da nuna cewa harin wani bangare ne na makircin kasa da kasa da na yanki bisa cikakkiyar masaniya da fahimtar kasashen duniya.
Sojojin kasar ta Sudan sun jaddada aniyarsu ta tunkarar wannan ta’addanci, ba tare da la’akari da irin makircin da ake kullawa ba, gami da tabbatar da aniyarsu ta kare ‘yancin kan kasa tare da goyon bayan al’ummar Sudan.