Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
Published: 30th, July 2025 GMT
Kwamandan, Nigerian Defence Academy NDA, Manjo Janar Abdul Khalifa Ibrahim ya bukaci dalibai da su jajirce wajen ganin sun samu nagartar ilimi.
Manjo Janar Abdul Khalifa Ibrahim ya yi wannan kiran ne a yayin bikin yaye dalibai da jawabai da kuma bayar da kyaututtuka da aka yi a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Malali Kaduna.
Kwamandan NDA wanda tsohon dalibi ne a kwalejin ya bayyana jin dadinsa da yadda dalibai ke gudanar da ayyukansu ya yabawa mahukunta da ma’aikatan FGC Kaduna bisa yadda suke kiyaye ka’idoji.
A nasa jawabin shugaban kungiyar tsofaffin dalibai ta FGC Kaduna, Kwamared Seyi Gambo ya ce kungiyar za ta ci gaba da bayar da gudummawar ta wajen daukaka darajar kwalejin ta hanyar daukar matakai na koyar da dalibai.
Shima da yake jawabi, shugaban taron kuma tsohon gwamnan jihar jigawa, Sanata Saminu Turaki ya bukaci dalibai da su tabbatar sun yi fice a fannin ilimi domin su zama masu amfani a cikin al’umma.
Shima da yake jawabi shugaban kwalejin gwamnatin tarayya ta Kaduna, Prince Adewale O. Adeyanju ya yi kira ga iyaye da su bada hadin kai ga hukumar makaranta domin ganin an kula da harkokin koyo.
An bayar da kyautuka na kyaututtuka da kudi ga daliban da suka kammala karatunsu da nagartattun dalibai da suka hada da malamai da suka kware sosai da kuma ma’aikatan da ba na koyarwa a kwalejin.
COV/SHETTIMA A.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Karatu Kwamandan Taron
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung
A wannan rana, a gun taron manema labarai da aka gudanar bayan kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC, Lee Jae-myung ya ce hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin Sin da Koriya ta Kudu yana da matukar muhimmanci, ya kuma yi imanin cewa birnin Shenzhen na kasar Sin zai karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC cikin nasara a shekara mai zuwa.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA