Aminiya:
2025-11-13@06:38:20 GMT

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 

Published: 30th, July 2025 GMT

Ruwan sama mai ƙarfi da ya sauka da safiyar ranar Laraba a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno, ya haddasa ambaliya.

Ruwan wanda ya fara sauka tun da misalin ƙarfe 5 na Asuba, ya cika tituna da gidaje musamman a unguwannin Dala, Bulunkutu, titin Damboa, filin Polo, da Federal Low Cost.

Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Ambaliyar ta haifar da cikas a rayuwar jama’a, inda ruwa ya lalata dukiyoyi mutane masu tarin yawa.

Mutane da dama dun fice daga gidajensu domin neman mafaka, musamman waɗanda gidajensu ruwa ya mamaye.

Hakazalika, wasu tituna sun shafe sakamakon mamakon ruwan, lamarin da ya hana mutane fita ko komawa gidajensu da kuma yin ayyukansu na yau da kullum.

Wasu daga cikin mazauna garin sun ce ambaliyar ta tsananta ne saboda magudanan ruwa sun cika da shara irin su robobi, datti da tarkacen kayan gini.

Hakan ya hana ruwa tafiya yadda ya kamata.

Wani da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce mafi yawan magudanan ruwan Maiduguri ba sa aiki yadda ya kamata saboda sun toshe da shara.

Ya ƙara da cewa rashin kula da tsaftar muhalli ne ya haddasa irin wannan matsala.

A halin yanzu, akwai buƙatar gwamnati ta ƙara sanya ido, ta tsaurara dokokin muhalli, da kuma wayar da kan jama’a kan muhimmancin tsaftar gari.

Har ila yau, akwai buƙatar a gyara magudanan ruwa domin gujewa irin wannan ambaliya a nan gaba.

Masana sun gargaɗi jama’a cewa ana sa ran samum mamakon ruwan sama a makonni masu zuwa.

Amma an buƙaci jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma haɗa kai da hukumomi domin shawo kan lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa magudanan ruwa ruwan sama

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa

Daga Khadijah Aliyu

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da Kwamitin Jagorancin Shirin Ilimi da Ƙarfafa Matasa a Arewa maso Yammacin Najeriya (EYEPINN) wanda kungiyar  Tarayyar Turai ke daukar nauyinsa domin fadada damar samun ingantaccen ilimi da kuma karfafa gwiwar matasa a yankin.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Kano, karkashin jagorancin Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda.

Yayin jawabinsa, Dakta Makoda ya bayyana shirin EYEPINN a matsayin Alƙawari mai Manufa”, yana mai cewa manufar shirin ita ce cike gibi a fannin ilimi, karfafa haɗin kai, da kuma baiwa matasa kwarewar da ta dace domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar.

Ya ce sabon kwamitin da aka kaddamar zai yi jagoranci kan dabaru, tsare-tsare, kulawa da tabbatar da gaskiya da inganci wajen aiwatar da ayyukan EYEPINN a fadin Kano.

Dakta Makoda ya kara da cewa, mambobin kwamitin sun haɗa da wakilai daga ma’aikatun gwamnati, hukumomi da cibiyoyi masu ruwa da tsaki, abokan hulɗa, da kuma wakilan Tarayyar Turai.

A yayin taron, abokan hulɗa ciki har da UNICEF, PLAN International, UNESCO, da kuma sashen nazari na ci gaban duniya (DIME) na Bankin Duniya, sun gabatar da jawabai da suka fayyace manufofi, da sakamakon da ake sa ran samu, da tsarin haɗin gwiwa, domin ƙarfafa tsarin samar da ilimi da kuma ƙarfafa matasa a Kano da ma yankin Arewa maso Yamma baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro
  • Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina
  • Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa
  • Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin