HausaTv:
2025-06-25@22:33:33 GMT

Sayyid Husi: Hare-haren Amurka Ba Za Su Yi Tasiri Akan Karfinmu Ba

Published: 4th, April 2025 GMT

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Al’ummar musulmi suna fuskantar manyan hatsari guda biyu,  da su ka hada laifukan da HKI take tafkawa a Gaza, da kuma kokarin shafe hakkokin falasdinawa baki daya.

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma tabo batun keta tsagaita wutar yaki da HKI take yi a kasar Lebanon yana mai kara da cewa, keta hurumin kasar Lebanon da ‘yan sahayoniyar suke yi, ya isa har birnin Beirut.

Akan kasar Syria ma, jagoran na kungiyar Ansarullah na Yemen ya yi ishara da hare-haren da ‘yan sahayoniya su ka kai  a cikin biranen Damascus, Hums da Dar’a.

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya ce,abokan gaba sun mayar da keta hurumin kasashen al’umma abinda za su rika yi kodayaushe. Haka nan kuma ya ce ko kadan bai kamata a mayar da kisan da ake yi wa Falasdinawa ya zama wani abu da ake gani yana faruwa a kowace rana ba.

Sayyid Abdulmalik ya yi kira da a sake dawo da fafutukar da ake yi a duniya baki daya, ta nuna kin amincewa da abinda yake faruwa a Gaza ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani

Akwai yiwuwar ƙasar Koriya ta Arewa mai ƙarfin makaman nukiliya za ta taimaka wajen gyara tashoshin nukiliyan Iran da hare-haren Amurka suka lalata da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya a Iran.

Wani masani mai suna Ankit Panda daga cibiyar zaman lafiya ta kasa da kasa ta da ke Amurka, ne ya bayyana hakan, baya Amurka ta kai hare-hare kan tashoshin nukiliya na ƙasar Iran.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito Ankit Panda, yana bayyana cewa matakin zai kawo ƙarshen irin takura da ƙasashen Yamma ke yi wa Iran.

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

Ta bayyana cewa, “Amurka da Isra’ila su ne kanwa uwar gani a rikici a yankin Gabas ta Tsakiya, sakamakon yake-yake da ƙoƙarin Isra’ila na faɗaɗa girman ƙasarta, tare sa smaun goyon bayan ƙasashen Yamma.

“Ya kamata al’ummomin duniya masu goyon bayan adalci su fito da murya ɗaya aula’anci wannan abin da Amurka da Isra’ila ke yi, kuma su taka musu burki,” in ji sanarwar da kamfanin dillancin labarai na Koriya ta Arewa (KCNA) ya ruwaito.

Ƙawancen soji tsakanin Iran da Koriya ta Arewa ta jima, kuma ana zargin ta taimaka musu wajen haɗawa da musayar makamai masu linzami masu gudun walƙilya masu cin dogon zango.

Ankit ya ce ba lallai ne Koriya ta Arewa ta taimaka wa Iran wurin ginawa ko hanzarta ƙera makaman nukiliya ba, domin gudun kada makaman su je Amurka. Idan hakan ya faru, Amurka na iya gano lagon fasahar makaman Koriya ta Arewar.

Amma dai akwai yiwuwar Koriya ta Arewar za ta iya, lura da yadda ke da ƙwarewa wajen fasahar makamai da kuma yadda a baya da yawaita taimako ta wannan bangare ga Rasha, wata babbar ƙawar Iran.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • ‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’
  • Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani