HausaTv:
2025-08-10@02:46:56 GMT

Sayyid Husi: Hare-haren Amurka Ba Za Su Yi Tasiri Akan Karfinmu Ba

Published: 4th, April 2025 GMT

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Al’ummar musulmi suna fuskantar manyan hatsari guda biyu,  da su ka hada laifukan da HKI take tafkawa a Gaza, da kuma kokarin shafe hakkokin falasdinawa baki daya.

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma tabo batun keta tsagaita wutar yaki da HKI take yi a kasar Lebanon yana mai kara da cewa, keta hurumin kasar Lebanon da ‘yan sahayoniyar suke yi, ya isa har birnin Beirut.

Akan kasar Syria ma, jagoran na kungiyar Ansarullah na Yemen ya yi ishara da hare-haren da ‘yan sahayoniya su ka kai  a cikin biranen Damascus, Hums da Dar’a.

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya ce,abokan gaba sun mayar da keta hurumin kasashen al’umma abinda za su rika yi kodayaushe. Haka nan kuma ya ce ko kadan bai kamata a mayar da kisan da ake yi wa Falasdinawa ya zama wani abu da ake gani yana faruwa a kowace rana ba.

Sayyid Abdulmalik ya yi kira da a sake dawo da fafutukar da ake yi a duniya baki daya, ta nuna kin amincewa da abinda yake faruwa a Gaza ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Yayin ziyararsa a kasar Indiya kwanan nan, shugaban kasar Philippines ya bayyana cewa, idan Sin da Amurka suka yi taho-mu-gama kan batun yankin Taiwan, Philippines ba za ta iya killace kanta daga ciki ba. Irin wannan furucin nasa yana da ban mamaki, wanda ya saba da alkawarin da Philippines ta yi na tsayawa ga manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, zai kara illata dangantakarta da kasar Sin, da zaman lafiya da tsaro a wannan shiyya.

Rura wutar rikici kan yankin Taiwan, yunkuri ne da Philippines ta yi na dogaro kan Amurka tare da ba ta hadin-kai, don hana ci gaban kasar Sin. Amma batun da ya shafi yankin Taiwan, batu ne na cikin gidan kasar Sin, kuma yadda za’a daidaita batun, harka ce ta al’ummar kasar zalla. Furucin shugaban Philippines ya saba da dokokin kasa da kasa da tsarin mulki na kungiyar ASEAN, tare da kawo babbar illa ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin shiyyar gami da muradun jama’ar Philippines. Mai yiwuwa dogaro kan Amurka zai iya kwantar da hankalin gwamnatin Marcos ta Philippines, amma hakikanin gaskiya shi ne, za ta girbi abun da ta shuka. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Mayar Da Dalibai 184 Da Suka Zo Hutu Daga Cyprus
  • Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin
  • Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Kasashen Kungiyar OIC Dangane Da Gaza
  • Shugaban Ansarullah Ya Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
  • Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya