Wani Kusa A Kungiyar Hamas Ya Yi Shahada A Wani Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon
Published: 5th, April 2025 GMT
An kashe wani kusa a kungiyar Hamas Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser, da wasu mutane biyu a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a wani gida a birnin Sidon, dake kudancin kasar Lebanon, a safiyar jiya Juma’a.
A cewar Al-Mayadeen, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai wani hari ta sama kan wani gida da ke birnin Sidon da ke kudancin kasar Lebanon, inda harin ya kashe babban kusa na Hamas Hassan Farhat da wasu mutane biyu daga cikin iyalansa.
A cewar rahoton, sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun kai hari a Al-Naqoura, Nabatiyeh, da Sidon a kudancin kasar Lebanon a yammacin ranar Alhamis, inda suka yi barna a yankunan da aka kai harin.
Shafin tashar “Russia Today” ya bayar da labarin cewa: Bisa kididdigar farko da aka yi, “Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser”, shugaban kusa a kungiyar Hamas, da dansa da ‘yarsa ne suka yi shahada a wani hari da jiragen Isra’ila suka kai a wani gida a yankin Dala’a a tsakiyar garin na Sidon. A wannan harin da aka kai ta hanyar amfani da jirgi maras matuki, an harba makamai masu linzami guda biyu a gidan.
Kawo yanzu kungiyar Hamas ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da shahadar Farhat ba, inda ta jaddada matsayinta na ci gaba da bin tafarkin neman ‘yanci wanda Farhat da iyalansa suka yi shahada a kansa.
Dangane da haka ne ma’aikatar lafiya ta kasar Labanon ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa akalla mutane uku ne suka rasa rayukansu wasu biyu kuma suka jikkata sakamakon wannan hari da jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai a birnin da ke kudancin kasar Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kudancin kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Ireland Ta Yi Dokar Hana Shigar Da Kayan Da Aka Kera A ” Isra’ila” Cikinta
Gwamnatin kasar Ireland ta yi doka a jiya Talata wacce ta hana a shigar da duk wasu kaya da aka kera a matsugunan ‘yan share wuri zauna da a karkashin dokokin kasa da kasa ake daukarsu a matsayin haramtattu.
Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Ireland ya fada wa kamfanin dillancin labaurn Faransa cewa; Gwamnati ta amince da a ci gaba da yin wasu dokokin da hana mu’amalar kasuwanci da matsugunan ‘yan share wuri zauna da ba su bisa doka, domin an yi su ne akan kasar Falasdinawa.”
Daga cikin kayayyakin da Majalisar dokokin ta Ireland ta haramta, da akwai ‘ya’yan marmari da itatuwa.
Ministan harkokin wajen Ireland Simon Harris ya fada wa ‘yan jarida cewa, yana fatan ganin matakin da karamar kasarsu ta dauka a kan Isra’ilan ya yi wa sauran kasashen nahiyar turai tasiri su bi sahu.”
Gwamnatin ta Ireland ta sanar da cewa; ta dogara ne da hukuncin kotun duniya ta manyan laifuka wacce ta fitar a watan Yuni na 2024.
A gefe daya kasashe turai da su ka hada Ireland, Spain da Norway sun bayyana aniyarsu ta amincewa da gwamnatin Falasdinu. Ita ma kasar Slovania ta bi sahun wadannan kasashen na turai, yayin da kasar Faransa ta bakin shugabanta Emmanuel Macro ta bayyana cewa; tana Shirin yin furuci da Daular Falasdinu.