Wani Kusa A Kungiyar Hamas Ya Yi Shahada A Wani Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon
Published: 5th, April 2025 GMT
An kashe wani kusa a kungiyar Hamas Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser, da wasu mutane biyu a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a wani gida a birnin Sidon, dake kudancin kasar Lebanon, a safiyar jiya Juma’a.
A cewar Al-Mayadeen, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai wani hari ta sama kan wani gida da ke birnin Sidon da ke kudancin kasar Lebanon, inda harin ya kashe babban kusa na Hamas Hassan Farhat da wasu mutane biyu daga cikin iyalansa.
A cewar rahoton, sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun kai hari a Al-Naqoura, Nabatiyeh, da Sidon a kudancin kasar Lebanon a yammacin ranar Alhamis, inda suka yi barna a yankunan da aka kai harin.
Shafin tashar “Russia Today” ya bayar da labarin cewa: Bisa kididdigar farko da aka yi, “Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser”, shugaban kusa a kungiyar Hamas, da dansa da ‘yarsa ne suka yi shahada a wani hari da jiragen Isra’ila suka kai a wani gida a yankin Dala’a a tsakiyar garin na Sidon. A wannan harin da aka kai ta hanyar amfani da jirgi maras matuki, an harba makamai masu linzami guda biyu a gidan.
Kawo yanzu kungiyar Hamas ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da shahadar Farhat ba, inda ta jaddada matsayinta na ci gaba da bin tafarkin neman ‘yanci wanda Farhat da iyalansa suka yi shahada a kansa.
Dangane da haka ne ma’aikatar lafiya ta kasar Labanon ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa akalla mutane uku ne suka rasa rayukansu wasu biyu kuma suka jikkata sakamakon wannan hari da jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai a birnin da ke kudancin kasar Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kudancin kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
Jami’an kasashen larabawa da na Musulmi sun bukaci daukar kwararan matakai kan Isra’ila bayan harin da ta kai a birnin Doha, inda suka bayyana harin a matsayin “na matsorata, da muggan laifuka.”
Da yake jawabi a gun taron ministocin harkokin wajen kasashen a birnin Doha, Sakatare-Janar na kungiyar kasashen Larabawa Ahmed Aboul Gheit ya ce harin, ha’inci ne da wauta.”
Sakatare-Janar na Kungiyar ya bayyana “cikakken goyon baya” ga Qatar bayan abin da ya kira “cin zarafin Isra’ila”, yana mai jaddada cewa dole ne kasashen duniya su dauki kwakkwaran mataki kan Tel Aviv.
Shi ma da yake jawabi a taron share fagen kasashen musulmin da na Larabawa, firaministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani ya yi tir da harin da ya danganta da na “ta’addancin kasa” da kuma keta duk wani yunkuri na shiga tsakani.”
Sheikh Abdulrahman Al Thani ya bukaci kasashen duniya da su daina yin Magana mai tamkar harshen damo, su kuma hukunta Isra’ila saboda “laifin” da ta aikata.
Ya yi wannan jawabi ne a wani taron share fage da aka yi a jajibirin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Musulunci da Qatar ta shirya bayan da Isra’ila ta kai wani hari irinsa na farko kan kasar a kan shugabannin Hamas a Doha. Yau Litinin ne shugabannin kasashen na Larabawa da na Musulmi zasu hadu a birnin Doha domin tattauna batun.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci