A wani muhimmin mataki na karfafa zaman lafiya da sulhu, gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamitocin zaman lafiya da sulhu a kananan hukumomin Jahun da Miga.

A lokacin bikin kaddamarwar, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, ya bayyana aikace-aikacen da aka dora wa kwamitocin.

Ya jaddada bukatar kwamitocin su gano musabbabin rikice-rikicen da suka addabi wasu sassan yankunan.

A cewarsa, wannan mataki yana nuna kudurin gwamnatin Gwamna Umar Namadi na tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’ummar jihar.

Ya ce an dora wa kwamitocin nauyin tantance tasirin wadannan rikice-rikice a tsakanin iyalai daban-daban, bayar da shawarwari masu inganci, tare da sanar da gwamnati duk wani muhimmin abu da ke bukatar daukar mataki.

Malam Bala Ibrahim ya ce, daya daga cikin manyan aikace-aikacen kwamitocin shi ne wayar da kan al’umma game da muhimmancin hadin kai da zama lafiya.

Ya kara da cewa, an kuma dora musu nauyin warware rikice-rikice ta hanyar sulhu tsakanin bangarorin da ke rikici.

Shugaban Kwamitin Karamar Hukumar Miga, DC Atiku Musa, ya bayyana godiyarsa bisa nadin da aka yi masa, tare da alkawarin gudanar da aikinsa bisa gaskiya da adalci don sauke nauyin da aka dora musu.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kwamitin Zaman Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?