A wani gagarumin ci gaba na inganta walwala da ci gaban yara da matasa wadanda suka isa makaranta, Shugaban Hukumar Kula da Ilimin Farko ta Jihar Nasarawa NSUBEB, Dokta Kasim Mohammed Kasim ya karbi tawagar Kids & Teens Resource Center K&TRC a wani taron bayar da shawarwari da aka mayar da hankali kan shirin Ilimi don Lafiya da walwala, wanda UNESCO ke tallafawa.

 

An gudanar da babban taron ne a hedkwatar Hukumar NSUBEB, inda ya samu halartar kwamishinonin hukumar su uku, da Daraktoci da dama, da kuma tawagar K&TRC karkashin jagorancin wanda ya kafa kuma Shugaba, Mista Martin-Mary Falana.

 

Tattaunawar a yayin zaman ta tabo batutuwan da suka shafi rayuwar yara da matasa a jihar, wadanda suka hada da yawaitar cin zarafin mata kamar lalata da fyade, cin zarafi a makarantu, kananan yara da auren dole, kaciyar mata, da kuma yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.

 

Mahalarta taron sun amince da bukatar gaggawar samar da cikakken martani ta bangaren ilimi domin tunkarar wadannan kalubale.

 

Shugaban hukumar ya yi alkawarin ba da cikakken kudurin siyasa na hukumar tare da ba da tabbacin baiwa kungiyar K&TRC na NSUBEB goyon baya wajen samar da yanayi mai dacewa don samun nasarar aiwatar da aikin.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), ta yi korafin cewa Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta mayar da yankin saniyar ware a kasafin ayyukan raya kasar da take yi a yankin.

Da yake jawabi yayin wani taron tattaunawa da ’yan kasa da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna ranar Talata, Shugaban Kwamitin Amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu (Wazirin Dutse), ya yi zargin cewa ana nuna wa yankin bambanci a muhimman manufofin gwamnati da kuma aiwatar da ayyukan raya kasa.

ACF ta ce hakan na faruwa ne duk da irin irin tarin gudunmawar da yankin ya ba gwamnatin mai ci a zaben 2023 da ya gabata.

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

Taron dai mai taken: “Nazarin alkawuran zabe: Inganta alakar gwamnati da ’yan kasa domin hadin kan kasa” ya tara gwamnoni da manyan masu rike da mukaman Gwamnatin Tarayya, ciki har da ministoci da sarakunan gargajiya da kuma kungiyoyin fararen hula.

A cewar wadanda suka shirya taron, an shirya shi ne domin karfafa fahimtar juna tsakanin mahukunta da kuma mutane a fadin arewacin Najeriya.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida mana cewa akwai yiwuwar Gwamnatin Tarayya ce ta hada kai da gidauniyar domin a fito da ayyukan gwamnatin a Arewa a daidai lokacin da ake ci gaba da korafin mayar da yankin saniyar ware.

Hakan, a cewar majiyoyin ba zai rasa nasaba da yadda aka ga tarin masu rike da mukamai a gwamnatin da kuma mambobin jam’iyyar APC mai Mulki suka halarci taron ba.

Daga cikin mahalarta taron dai akwai akwai wakilin Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da Mai ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu da kuma Gwamnonin Kaduna (Uba Sani), Gombe (Muhammad Inuwa Yahaya) da Kwara (AbdulRahman AbdulRasaq).

Daga cikin Ministocin da suka sami halartar taron kuwa akwai na Tsaro, Badaru Abubakar, da Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle da na Yada Labarai, Mohammed Idris, da Karamin Ministan Ayyuka, Muhammed Bello Goronyo da Karamin Ministan Gidaje, Yusuf Abdullahi Ata da kuma Karamar Ministar Abuja, Mariya Mahmud Bunkure.

Sauran sun hada da Babban Hafsan Tsaro na Najeriya, Christopher Musa da Babban Hafsan Sojojin Sama, Hassan Abubakar da kuma shugabar hukumar kula da shige da fice ta Najeriya, Kemi Nandap.

Akwai kuma tsofaffin Gwamnoni irin su Ramalan Yero (Kaduna), Aliyu Sjinkafi (Zamfara), Ibrahim Shekarau (Kano) da Mu’azu Babangida Aliyu (Neja) da dai sauransu.

Sai dai ko kafin taron na ranar Talata, ko a makon da ya gabata sai da tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar Shugaban Kas ana jam’iyyar NNPP. Azaben 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi irin wannan zargin cewa gwamnatin Tinubu na fifita kudanci a kan arewaci a fannin ayyukan raya kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000