Al-Azhar ta yi kira da a kama Netanyahu a matsayin mai laifin yaki
Published: 5th, April 2025 GMT
Cibiyar da ke sa ido kan tsattsauran ra’ayi da ke karkashin cibiyar ilimi ta Al-Azhar ta Masar, ta fitar da wata sanarwa da ta yi kira da a kame firaministan Haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu a matsayin mai laifin yaki.
Shafin sawtbeirut.com ya bayar da rahoto kan sanarwar da ke cewa, cibiyar yaki da tsattsauran ra’ayi ta Al-Azhar, ta yi Allah wadai da tarbar da kasar Hungary ta yi wa firaministan Isra’ila, wanda ke fuskantar sammaci na kasa da kasa da kotun ICC ta bayar, ta kuma sanar da cewa: “Manufar wannan mataki shi ne tauye matsayin kotun kasa da kasa da kuma keta hurumin ta.
Sanarwar ta ce: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa alama ce ta tabbatar da adalci a duniya, kuma dole ne kasashen duniya su hada kai wajen mara mata baya wajen hukunta masu aikata laifukan yaki.
Kungiyar ta bayyana cewa: shawarwarin kasa da kasa da hukunta wadanda suka aikata laifukan yaki shi ne ginshikin tabbatar da zaman lafiya da adalci, kuma mutane suna da daidaito a gaban doka, babu wani wanda yake a birbishinta.
Sanarwar ta ce: “Babu lokacin yin shiru kana bin da yake fruwa, domin yin shiru yana halasta sabbin laifuka, kuma Gaza ta kasance share fage ne kawai ga ci gaba da aiwatar da bakaken manufofi da zubar da jini, da kashe rayuka.
An fitar da wannan sanarwa ne bayan da kasar Hungary ta yi maraba da firaministan Isra’ila duk da cewa kotun kasa da kasa ta bayar da sammacin kama shi.
A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Benjamin Netanyahu bisa zargin aikata laifukan yaki da cin zarafin bil adama a Gaza.
Duk da wannan hukuncin, Netanyahu ya isa kasar Hungary inda ya gana da firaministan kasar Viktor Orban.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
Ya bayyana cewa, ziyarar da ya kai a tashar ruwa ta PTML da Tin Can na da nufin sanin irin kalubalen da jami’an sa ke fuskanta wurin amfani da sabuwar na’urar zamani domin binciken kayayyakin da ake shigowa da su kasar.
Ya kuma kara gargadin jama’a game da karuwar kwararowar magunguna kasar da ba su da rajista, musamman magungunan inganta jima’i, inda ya yi gargadin cewa irin wadannan abubuwa na da matukar barazana ga kiwon lafiyar jama’a.
Ya yi gargadin cewa, yin amfani da wadannan magungunan ba tare da kulawar likitoci ba zai iya haifar da mummunar illa ga lafiyar jiki, ciki har da haɗarin cututtukan zuciya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp