Jagora: Iran, Tabbas Zata Ki Amincewa Da Tattaunawa Da Kasashe Masu Girman Kai
Published: 8th, March 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran Imam Ayatullah sayyid Aliyul Kahaminae, ya bayyana cewa tursasawa kasar Iran ta shi tattauna da gwamnatin Amurka ba abin amincewa ba ne, kuma yin hakan ba zai warware matsalolin da ke tsakaninsu ba.
Tashar talabijinta Presstv a nan Iran ta nakalto Jagoran ya na fadar haka a yau Asabar a lokacin da yake ganawarsa, da shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan da alkalin al-kalan kasa Muhsen Ejei da kuma shugaban majalisar dokokin kasar Muhammad Bakir Qalibof da kuma wasu jami’an gwamnatin kasar da dama a gidansa.
Jagoran ya kara da cewa ba matsalar makamashin Nukliya ne suke bukatar tattaunawa da Iran ba, sai dai suna su tilastawa kasar Iran ra’ayinsu, a cikin dukkan al-amuran kasar. Don haka a yanke gwamnatin JMI ba zata amince da shishigi a cikin al-amuran kasar ba.
Jagoran ya zargi kasashen Turai da rashin cika alkawulansu a cikin shirin Nukliyar kasar, sannan da yi mata kariya ba tare da jin kunya ba.
Idan su na zargin Iran da rashin cika alkawula a sherin makamashin Nukliyarta? to su, sun cika alkawula ne, a shirin shirinta na Makamancin Nujkliyar?
Don haka turawan ne suka fara saba alkawulan da suka dawkawa kasar Iran, musamman bayan da Amurka ta janye daga yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, a shekara ta 2018.
A lokacin turawan sun sha sha’alwashin kyautata al-amura amma sun kasa cikasu.
Yace Iran ba zata taba dogaro da kasashen yamma a al-amura masu muhimmanci ga ci ga mutanen kasar ba.
Kuma irana ba zata bar duk wani abu na ci gaban kasar, don tsaron wata kasa a duniya ba.
Ya kuma zargi kasashen yamma ga ba da ya da fuska biyu, musamman kan abinda ya shafi watsa labarai. Daga karshe ya ce, Ya ce Iran ba zata bar wata kasa ta yi shishiga cikin al-amuranta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa addinin musulunci ya daukaka matsayin macce ya kuma bada matsayin guda da maza a fagagen zamantakewa da siyasa, ya kuma yi watsi ya akidar kasashen yamma wadanda suka kaskasntata suka maida ita kayan aika don cimma bukatatun wasu.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a taron dubban mata daga yankunan daban daban na kasar a yau laraba a nan Tehran.
Imam Khaminae ya ce, mata a Iran suna koikoyon Fatimah Azzahra (s) diyar manzon Allah (s) don haka suka kama hanyar daukaka wanda alah ya bawa mata. Fatima (s) makaranta ce ga mata kuma daukaka ce a garesu.
Imam Khaminae ya ce aladun kasashen yamma da kuma tsarin jarin hujja dangane da mata ba amintaccene a addinin musulunci ba. Yace tsare-tsaren da addinin musulunci ya zo da su na, hijabi da hana cakudar mata da maza a tarurruka, da kudaitar da aure da sauransu duk don kare Martaban mata ne a mataki na farko. Yace musulunci bai hana mata shiga a dama da su a cikin al-amuran zamantake da siyasa da sauransu ba, amma tare da kiyaye mutuncinta, da aikita na asali wanda shi ne kula da iyala da tarbiyyan yayanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI December 3, 2025 An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci