HausaTv:
2025-11-23@09:43:19 GMT

Jagora: Iran, Tabbas Zata Ki Amincewa Da Tattaunawa Da Kasashe Masu Girman Kai

Published: 8th, March 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran Imam Ayatullah sayyid Aliyul Kahaminae, ya bayyana cewa tursasawa kasar Iran ta shi tattauna da gwamnatin Amurka ba abin amincewa ba ne, kuma yin hakan ba zai warware matsalolin da ke tsakaninsu ba.

Tashar talabijinta Presstv a nan Iran ta nakalto Jagoran ya na fadar haka a yau Asabar a lokacin da yake ganawarsa, da shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan da alkalin al-kalan kasa Muhsen Ejei da kuma shugaban majalisar dokokin kasar Muhammad Bakir Qalibof da kuma wasu jami’an gwamnatin kasar da dama a gidansa.

Jagoran ya kara da cewa ba matsalar makamashin Nukliya ne suke bukatar tattaunawa da Iran ba, sai dai suna su tilastawa kasar Iran ra’ayinsu, a cikin dukkan al-amuran kasar. Don haka a yanke gwamnatin JMI ba zata amince da shishigi a cikin al-amuran kasar ba.

Jagoran ya zargi kasashen Turai da rashin cika alkawulansu a cikin shirin Nukliyar kasar, sannan da yi mata  kariya ba tare da jin kunya ba.

Idan su na zargin Iran da rashin cika alkawula  a sherin makamashin Nukliyarta? to su, sun cika alkawula ne, a shirin shirinta na Makamancin Nujkliyar?

Don haka turawan ne suka fara saba alkawulan da suka dawkawa kasar Iran, musamman bayan da Amurka ta janye daga yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, a shekara ta 2018.

A lokacin turawan sun sha sha’alwashin kyautata al-amura amma sun kasa cikasu.

Yace Iran ba zata taba dogaro da kasashen yamma a al-amura masu muhimmanci ga ci ga mutanen kasar ba.

Kuma irana ba zata bar duk wani abu na ci gaban kasar, don tsaron wata kasa a duniya ba.

Ya kuma zargi kasashen yamma ga ba da ya da fuska biyu, musamman kan abinda ya shafi watsa labarai. Daga karshe ya ce, Ya ce Iran ba zata bar wata kasa ta yi shishiga cikin al-amuranta ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro

Gwamnatin Jihar Kwara ta bayar da umarnin rufe makarantu a ƙananan hukumomin jihar guda huɗu na saboda ƙaruwar hare-hare a jihar cikin sa’o’i 48 da suka gabata.

Aƙalla mutane uku sun mutu a garin Bokungi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a ranar Laraba.

Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka

Lamarin ya faru kasa da sa’o’i 24 bayan mummunan harin da aka kai coci a Eruku, Ƙaramar Hukumar Ekiti ta jihar, inda aka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da mutum 30.

Majiyoyin al’umma sun ce an fara yin garkuwa da mutane huɗu, ciki har da ɗan sa-kai, a cikin waɗannan hare-haren.

Ɗaya daga cikin majiyoyin ya ce maharan daga baya sun kashe manoman shinkafa biyu tare da jikkata wani mutum na uku wanda aka ce ɗan sa-kai ne.

A halin yanzu, gwamnati ta ce ta ɗauki matakan tsaro na musamman a makarantu, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinta na tabbatar da kariya ga ɗalibai.

Matakan dai sun shafi makarantu a ƙananan hukumomin Ifelodun, Ekiti, Irepodun, Isin, da Oke Ero.

Gwamnatin ta ce wannan mataki ya nuna ƙudurinta na dakile ayyukan masu garkuwa da mutane waɗanda za su iya amfani da ɗalibai a matsayin garkuwa daga matsin lambar da suke fuskanta.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi da Ci gaban Ɗan Adam na jihar, Dr Lawal Olohungbebe, ya fitar, ya ce matakan sun shafi makarantun kwana a Irepodun.

Sanarwar ta ƙara da cewa matakin zai ci gaba da kasancewa a yankunan har sai an samu cikakken tabbacin tsaro kafin a dawo da harkokin yau da kullum.

A ranar Litinin, ’yan bindiga sun kai hari a makarantar GGCSS Maga, Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu ta Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum ɗaya tare da yin garkuwa da ɗalibai 25.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: HKI Na Faskantar Mummunan Aikin Leken Asiri Daga Kasar
  • Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa
  • Gwamnatin Neja Ta Rufe Makarantu Saboda Matsalar Tsaro
  •  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  •  Iran Tana Cikin kasashe 10 Na Farko Da Su Ka Fi Yawan Wuraren Tarihi
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro