HausaTv:
2025-07-13@06:21:52 GMT

Jagora: Iran, Tabbas Zata Ki Amincewa Da Tattaunawa Da Kasashe Masu Girman Kai

Published: 8th, March 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran Imam Ayatullah sayyid Aliyul Kahaminae, ya bayyana cewa tursasawa kasar Iran ta shi tattauna da gwamnatin Amurka ba abin amincewa ba ne, kuma yin hakan ba zai warware matsalolin da ke tsakaninsu ba.

Tashar talabijinta Presstv a nan Iran ta nakalto Jagoran ya na fadar haka a yau Asabar a lokacin da yake ganawarsa, da shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan da alkalin al-kalan kasa Muhsen Ejei da kuma shugaban majalisar dokokin kasar Muhammad Bakir Qalibof da kuma wasu jami’an gwamnatin kasar da dama a gidansa.

Jagoran ya kara da cewa ba matsalar makamashin Nukliya ne suke bukatar tattaunawa da Iran ba, sai dai suna su tilastawa kasar Iran ra’ayinsu, a cikin dukkan al-amuran kasar. Don haka a yanke gwamnatin JMI ba zata amince da shishigi a cikin al-amuran kasar ba.

Jagoran ya zargi kasashen Turai da rashin cika alkawulansu a cikin shirin Nukliyar kasar, sannan da yi mata  kariya ba tare da jin kunya ba.

Idan su na zargin Iran da rashin cika alkawula  a sherin makamashin Nukliyarta? to su, sun cika alkawula ne, a shirin shirinta na Makamancin Nujkliyar?

Don haka turawan ne suka fara saba alkawulan da suka dawkawa kasar Iran, musamman bayan da Amurka ta janye daga yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, a shekara ta 2018.

A lokacin turawan sun sha sha’alwashin kyautata al-amura amma sun kasa cikasu.

Yace Iran ba zata taba dogaro da kasashen yamma a al-amura masu muhimmanci ga ci ga mutanen kasar ba.

Kuma irana ba zata bar duk wani abu na ci gaban kasar, don tsaron wata kasa a duniya ba.

Ya kuma zargi kasashen yamma ga ba da ya da fuska biyu, musamman kan abinda ya shafi watsa labarai. Daga karshe ya ce, Ya ce Iran ba zata bar wata kasa ta yi shishiga cikin al-amuranta ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bakai yayi tir da gwamnatin Amurka kan takunkuman da ta dorawa Francesca Albanese jami’a Ta musamman a hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD wacce take aikin tattara bayanai dangane da yakin da ke faruwa a Gaza.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Bakaei yana fadar haka a shafinsa na X ya kuma kara da cewa ; Ba wanda ya isa ya rufe bakin gaskiya. Ya ce gwamnatin kasar Amurka ta dorawa malama Francesca Albanese takunkumi ne saboda fadin gaskiya. Saboda tsayawa kan cewa Natanyahu yana aikata kisan kiya shi a gaza. Ya na kashe yara kanan da mata. Kuma ta sha bada shawarwari ga hukumar kare hakkin bil’adama na MDD na a kori HKI daga hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tana Nazarin Sakon Amurka Na Bukatar Farfado Da Tattaunawa Shirin Makamashin Nukliya Na kasar
  • Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD
  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
  • Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Jagora Da Kansa Ya Shiga Dakin Ba Da Umarnin Sojin Lokacin Yaki
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali