HausaTv:
2025-07-11@09:27:43 GMT

Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran

Published: 8th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammad Bin Abdurrahman Al-Thani, ya kara nanata matsayin kasar na kin duk wani yaki kan shirin Nukliyar kasar Iran, ya kuma yi kira ga Amurka da Iran su warware wannan matsalar ta ruwan sanyi. Ko hanyar diblomasiyya.

Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa shirinta na makamashin na zaman lafiya ne.

Sannan don haka ne ta amince ta kulla yarjeniyar shirin nukliya ta zaman lafiya  da manya manyan kasashen duniya, a shekara ta 2015 daga ciki har da kasar Amurka. Amma shugaban kasar Amurka na lokacin Donql Trump ta fidda kasar daga yarjeniyar sannan ta dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni don tursasa mata ta sake zama don sabuwar tattaunawa da ita.

Mohammed bin Abdulrahman Al Thani yace “akwai bukatar kasashen Iran da Amurka su fahinci juna a cikin wannan batun” sannan ya sake nanata cewa Qatar bata goyon bayan yaki. Sannan daga karshe yace matsalar nukliyar kasar Iran ta zama abinda damuwa ga dukkan kasashen yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Ban da haka, bayan da aka tsara “shirin shekaru 5”, yana da muhimmanci a aiwatar da shi. A kasar Sin, bayan da aka gabatar da wani “shiri na shekaru 5”, dole ne a aiwatar da shi yadda ake bukata. Kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da majalisar gudanarwar kasar za su tsara salon aiwatar da dukkan ayyuka, da raba su ga sassa da yankuna daban-daban, don a aiwatar da su a matakai daban daban. Bayan haka, hukumomi daban daban su kan gudanar da ayyukan sa ido a tsakiyar wa’adin shirin, kuma za a tantance ainihin sakamakon da aka samu bayan karewar shirin.

Ta wadannan halayen musamman, za a iya ganin abubuwan da za su tabbatar da aiwatar da shirin na raya kasa: Na farko, kokarin kare muhimman muradun jama’a, da tabbatar da yanke shawara ta wata hanya mai dacewa, kuma bisa tsarin dimokuradiyya. Na biyu, yin amfani da tsare-tsaren shari’a wajen tabbatar da ingancin shirin da aka tsara, da mai da shi karkashin sa ido da aka yi masa. Na uku, tun daga gwamnatin tsakiya zuwa kananan hukumomi, dole ne a aiwatar da shirin raya kasa a tsanake, domin tabbatar da cimma burin da aka sanya a gaba. A cikin wadannan abubuwa, ana iya ganin ruhin dimokuradiyya da bin doka da oda, da kuma yanayin aiki na mai da hankali, da nuna sanin ya kamata, wadanda suka kasance tushen ci gaban kasar Sin.

A cewar mista Peterside, ta hanyar koyi da fasahohin kasar Sin, Najeriya za ta iya cin gajiyar dimbin albarkatun kasa da take da su, don tabbatar da cikar burinta na raya tattalin arziki. Ni ma na yi imanin cewa, Najeriya za ta iya yin hakan, tare da samun biyan bukata. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso
  • Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya