‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja
Published: 8th, March 2025 GMT
“Wadanda aka samu da laifi doka za ta hukunta su.
“Ayyukan sun kai ga kwato tarin muggan makamai, haramtattun abubuwa, da abubuwan da ke da alaka da aikata laifuka.
Wadannan sun hada da busasshen ganyen da ake zargin tabar wiwi ne, gatari uku da adduna uku, wadanda galibi ake amfani da su wajen aikata munanan laifuka.
“Kananan bututu guda shida na manne, bongs din hannu guda biyar, kayan da aka fi hadawa da abubuwan maye, almakashi guda takwas, katunan ID guda biyar, kananan kwantena na filastik da yawa da wasu kwayayen da ake zargin haramun ne.
“Rundunar ta kuma kara sanya ido kan gine-ginen da aka yi watsi da su da kuma wuraren da aka gano a matsayin maboyar masu aikata laifuka.
“Rahotanni na leken asiri sun nuna cewa ana amfani da wasu daga cikin wadannan gine-gine don ayyukan haram, wadanda suka hada da shan muggan kwayoyi da kuma aikata laifuka.
“Don magance wannan al’amari, an tsaurara matakan tsaro a kan irin wadannan gine-gine, an kuma kai samame da dama tare da wanke su ba bisa ka’ida ba.
“An shawarci masu kadarorin da su tsare gine-ginensu don hana yin amfani da su, yayin da ake karfafa hukumomin gwamnati da su hanzarta daukar matakan da suka dace don magance wannan damuwa.
“Kwamishanan ‘yansanda na rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, CP Olatunji Disu, ya tabbatar wa dukkan mazauna yankin kudurinsu na tabbatar da tsaro da tsaro.
“An yi kira ga jama’a da su sanya ido tare da gaggauta kai rahoton duk wani abu da ake zargi ga ‘yansanda ta hanyar tuntubar gaggawa kamar haka:- 08032003913, 08028940883, 07057337653, Sashin amsa korafi: 08107314192.
“Rundunar ‘yan sanda ta FCT ta ci gaba da himma wajen samar da tsaro a cikin al’umma, kuma za mu ci gaba da daukar kwararan matakai kan duk wani nau’in aikata laifuka.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.
Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.
Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.
Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.
Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.
Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA