Leadership News Hausa:
2025-08-12@12:47:37 GMT

Yadda Ake Ayyukan Gina Ababen More Rayuwa A Jihar Zamfara 

Published: 6th, March 2025 GMT

Yadda Ake Ayyukan Gina Ababen More Rayuwa A Jihar Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, ziyarar wani bangare ne na tsarin Gwamna Dauda Lawal na tabbatar da ingantattun ayyuka a faɗin jihar da kuma tabbatar da kammala ayyukan a kan lokaci.

 

“A ranar Talata ne Gwamna Dauda Lawal ya fara ziyarar aiki domin duba ɗimbin ayyukan da gwamnatinsa ta fara aiwatarwa.

 

“An fara ziyarar ne da Babban Asibitin Gusau, ɗaya daga cikin manyan asibitocin da aka gyara, tare da samar mata da kayan aiki a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

A lokacin da yake duba aikin filin jirgin sama na Zamfara, Gwamna Lawal ya ce, gwamnatinsa ba wai kawai tana gina kowane irin filin jirgin saman ba ne, amma ana ginin ne na zamani wanda zai yi fice bisa ga dukkan alamu.

 

“Gwamnan ya nuna jin daɗinsa da yadda aikin ke gudana, wanda ya haɗa da titin jirgi da tasha.

 

“Gwamna Lawal ya kuma duba hanyar garin Rawayya da ke gudana da kuma aikin gina tsohuwar Titin Kasuwa zuwa mahaɗar Chemist na Nasiha.

 

“Sauran ayyukan da Gwamna Dauda Lawal ya duba a halin yanzu sun haɗa da gyaran kashi na biyu na Sakatariyar JB Yakubu ta Jihar, Kwalejin Kimiyya ta Zamfara (ZACAS), da kuma Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi

Gwamnatin jihar Kano ta amince da korar wasu manyan mataimaka na musamman (SSAs) ba tare da bata lokaci ba, sakamakon zarge-zargen da wasu kwamitocin bincike suka yi na gudanar da bincike kan wasu laifuka.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya fitar.

 

A wani gagarumin mataki da gwamnan ya dauka, ya amince da korar Abubakar Umar Sharada, babban mataimaki na musamman kan harkokin siyasa, bayan da kwamitin bincike na musamman ya tuhume shi a matsayin wanda ya shirya belin wani mai hatsarin gaske kuma dilan kwyaan maye, Sulaiman Aminu Danwawu, wanda ya tabbatar da laifin Abubakar Sharada a cikin takaddamar belin ta hanyar kwamitin da ya gabatar a gaban kwamitin.

 

A cewar wata wasika da ya fitar a ranar Juma’a, 8 ga watan Agusta 2025, ta hannun sakataren gwamnatin jihar (SSG), Sharada an umurce shi da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannun sa ga babban sakatare, bincike, ranar Litinin, 11 ga Agusta 2025.

 

An kuma gargade shi da kada ya nuna kansa a matsayin jami’in gwamnati a wannan gwamnati mai ci.

 

Hakazalika, gwamnan ya sauke Tasiu Adamu Al’amin Roba, babban mataimaki na musamman, daga mukaminsa bayan kama shi da laifin sama da fadi da wasu buhunan hatsi a wani dakin ajiyar kaya da ke Sharada a shekarar 2024.

 

Tuni dai Roba ya gurfana a gaban kotu inda ake tuhumarsa da laifin sata da hada baki a kan zargin karkatar da kadarorin jama’a.

 

Haka kuma an umurci Tasiu Adamu Al’amin Roba da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannun sa da suka hada da katin shaida a ranar Litinin ko kuma kafin ranar Litinin 11 ga watan Agusta 2025. Ya kuma yi gargadin kada ya bayyana kansa a matsayin ma’aikacin gwamnati a wannan gwamnati mai ci.

 

A wani labarin kuma, gwamnatin jihar ta wanke Hon. Musa Ado Tsamiya, mai ba shi shawara na musamman kan magudanun ruwa, wanda kwamitin bincike ya wanke shi daga dukkan zarge-zargen, inda ya tabbatar da cewa ba shi da laifi.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na tabbatar da adalci da kuma rashin hakuri da cin hanci da rashawa, yana mai gargadin dukkanin jami’an gwamnati da su kasance masu bin ka’ida mai inganci a ayyukansu da kuma rayuwarsu ta sirri.

 

A cikin wannan sanarwa, ana shawartar jama’a da kada su yi wata hulda da wadannan ‘yan siyasa biyu da aka kora a kan duk wani batu da ya shafi gwamnatin jihar Kano, duk wanda ya yi haka, ya yi ne a kan kansa.

 

 

 

Saki/Abdullahi jalaluddeen/Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
  • Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
  • Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Maniyyatan Aikin Hajjin 2026 Su Fara Biyan Kudaden Ajiya
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai
  • Za A Inganta Fannin Lafiya Da Sauran Ababen More Rayuwa A Sule Tankarkar