Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-01@04:56:00 GMT

Rasha Ta Kai Hari Mahaifar Shugaban Ukraine Zelensky

Published: 6th, March 2025 GMT

Rasha Ta Kai Hari Mahaifar Shugaban Ukraine Zelensky

Jami’ai a Ukraine sun ce mutane huɗu sun mutu, 29 da suka jikkata, a wani harin makami mai Linzami da Rasha ta kai kan wani Otel a birnin Kryvyi Rih – Mahaifar shugaba Zelensky.

 

Masu aikin ceto na ƙoƙarin zaƙulo masu sauran numfashi a ɓaraguzan gine-gine.

 

Wannan hari na zuwa ne sa’o’i bayan Amurka ta tabbatar da cewa ta daina musayar bayanan sirri da Ukraine — wanda haka zai kasance ƙalubale matuƙa ga Ukraine wajen iya daƙile hare-haren Rasha.

 

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce masu aikin sa kai daga wata ƙungiyar bayar da agaji daga Amurka da Birtaniya na daga cikin waɗanda harin ya rutsa da su a daren jiya.

 

Hakazalika, an kai wasu hare-haren birnin Odesa wanda ya yi sanadiyyar jikkata mutum biyu da lalata manyan gine-gine biyu, kamar yadda gwamnan yankin, Oleh Kiper ya tabbatar.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Rasha Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

“Ya zamar mana wajbi, mu kulla wannan hadakar, musamman domoin mu tabbatar da cewa, mun tsaftace tsarin,” Inji Dantsoho.

Ya kara da cewa, wannan aikin, ba wai kawai za kara habaka samar da kariya da kuma kara ingnata tsaro bane, har da kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara ciyar da tattalin arzikin kasar nan gaba.

A cewar Shugaban, cunkoson da ake samu a Tashar ta Tin Can Island na ci gaba da haifar da jinkiri da rashin gudanar da ayyuka yadda suka kamata da kuma rage gudanar da hada-hadar kasuwanci, yadda ta kamata, wanda kuma hakan, ke janyowa kara habaka tattalin arzikin kasar.

Dantsoho wanda Babban Janar Manaja na sashen kula da tsaro a Hukumar ta NPA Mista Anthony Edosomwan ya wakilce shi a wajen kaddamar da aikin ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin ne, zuwa kwana uku, musamman domin a samu nasarar gudanar da aikin.

Shugaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ya wallafa a kafafen yada labarai, kan sanarwar wayar da kan jama’a kan batun mahimmancin, tsaftace Tashar ta Tin Can Island.

“Wannan wani mataki ne, da aka samu goyon bayan masu ruwa da tsaki ciki har da masu yin amfani da Tashar da ‘yan kasuwa da kuma sauran alummar da ke a kusa da yankin”, A cewar Dantsoho.

Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA ba za ta yi kasa a guiwa, wajen kara mayar da hankali da kuma zagewa, domin ta samu cin nasara wajen tabbatar da tsaftace muhalli da kuma samar da kyakyawan yanayi, a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ba.

“Yanayi na samun gurbatacciyar Iska da kutsen da ake yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, abu ne da Hukumar ta NPA, ba za ta rungume hannu ta bari ba, ” Inji Dantsoho.

“Wannan aikin na tsafrace Tashar ba wai kawai na da alfanu ga ayyukan da ake gudanarwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar bane, hatta alumomin da suke daura da Tashoshin, suma zai yi masu alfanu,“ A cewar Shuaban .

Shuaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ta NPA da faro shi a wannan shekarar ta 2025, na daga cikin shiryae-shiryen rage cunkoso da kuma samar da saukin gudanar da ayyuka, Hukumar ta NPA, wanda hakan zai taimaka matuka wajen samar da kyakywar makoma ga Tashoshin Jiragen Ruwa, da ke a daukacin kasar nan.

A cewar Shugaban, wannan hadakar da sauran jami’an tsaro da kuma yin gangamin na wayar da kan alumma, Hukumar na bukatar goyon bayan alumma, dominn ta samu nasarar, aikin da ta sanya a gaba,

“A saboda haka, Mahukuntan Hukumar ta NPA, na bukatar goyon baya da hadin kan jama’a musamman domin a samar da kyakyawan yanin da ya dace a Tashar Jirgin Ruwan,” A cewar Shugaban.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 20 sun rasu a hatsari motar ’yan wasan Jihar Kano
  • Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja 
  • Daesh ta yi ikirarin kai hari kan gwamnatin Syria
  • Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba