Sibil Difens za ta da ɗauki sabbin ma’aikata
Published: 6th, March 2025 GMT
Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) ta samu sahalewar Shugaban Ƙasa na ƙara daukar sabbin ma’aikata.
Babban Kwamandan Hukumar, Ahmed Aifi, na ya sanar da haka, a yayin ƙaddamar da Baban Ofishin Yanki na Hukumar a Ƙaramar Hukumar Bwari da ke yankin Babban Birnin Tarayya a ranar Laraba.
“Nan gaba kaɗan za mu ɗauki ’yan Najeriya masu kyawawan ɗabi’u a matsayin jami’ain Sibil Difens, kuma muna godiya ga shugaban ƙasa bisa wannan dama da ya ba hukumar,” in ji shi.
Ya bayyana cewa Hukumar ta fara shirye-shiryen ɗaukar sabbin, amma sai nan gaba za ta sanar da ranar fara ɗaukar tasu.
An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?Ya kuma yaba wa Majalisar Ƙaramar Hukumar Bwari bisa gina ofishin, wanda ya ce zai taimaka wajen inganta tsaro.
Olusola Odumosu, wanda shi ne Kwamandan Hukumar, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar, John Gabata da ya samar da ofishin cikin kyakkyawan yanayi ga jami’an hukumar tsaron.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bwari daukar sabbin jami ai Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.
Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.
Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu KanoShugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.
Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.
Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.
Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.
Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.
Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.
NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.
Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.
Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.
Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.