Ayukkan Sojoji Na Taimakawa Wajen Samar da Tsaro a Taraba
Published: 6th, March 2025 GMT
Kwamandan runduna ta 6 ta sojan Nijeriya a jihar Taraba, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya karbi bakuncin mahalarta kwas din Cibiyar Bayar da Agaji ta Sojojin Najeriya (NARC) karo na 7/2025 a wani rangadin karatu a jihar Taraba a hedkwatar rundunar dake Jalingo.
A yayin ziyarar, Janar Uwa ya yi wa mahalarta taron karin haske kan ayyukan gudanar da aiki, nasarori, kalubale, da hasashen da za a yi a nan gaba, inda ya bayyana muhimman nasarorin da aka samu wajen yaki da rashin tsaro a cikin shekarar da ta gabata.
Ya yi nuni da cewa al’amuran satar mutane don neman kudin fansa, fashi da makami, da kuma rikicin kabilanci ya ragu matuka saboda jajircewar sojojin.
A wani bangare na bayanin, Janar Uwa ya baje kolin makamai da alburusai da aka kwato daga ayyuka daban-daban da aka samu nasara.
Ya yaba da kwazo da jajircewar sojojin, wanda jajircewarsu ya taimaka matuka wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
A nasa jawabin, shugaban tawagar, Manjo Janar Dahiru Sanusi, wanda ya wakilci Darakta Janar na NARC, Manjo Janar Garba Ayodeji Wahab murabus, ya bayyana godiya ga kwamandan da jami’ansa bisa kyakkyawar tarba da karimcin da suka yi.
Ya yi nuni da cewa, an shirya rangadin binciken ne domin fahimtar aiki da kuma aikace-aikace na zahiri, tare da mayar da hankali musamman kan tantance tasirin ayyukan tsaro na rundunar ga kanana da matsakaitan masana’antu (SMEs) a cikin jihar.
Za a ci gaba da rangadin ne tare da ziyartan wasu muhimman wurare a fadin jihar ta Taraba, domin baiwa mahalarta damar fahimtar yanayin tsaro da kuma rawar da sojojin Najeriya ke takawa wajen samar da kwanciyar hankali da tsaro.
PR/ Sani Sulaiman
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.
Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.
Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.
Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.
Usman Muhammad Zaria