Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@22:42:23 GMT

Gwamna Zamfara Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikata.

Published: 6th, March 2025 GMT

Gwamna Zamfara Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikata.

 

Gwamna Dauda Lawal ya amince da nadin Yakubu Sani Haidar a matsayin babban shugaban ma’aikatan jihar Zamfara.

 

Nadin wanda ke fara aiki nan take, ya fito ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar (SSG), Malam Abubakar Mohammad Nakwada, ta bakin babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Sulaiman Ahmad Tudu.

 

A cewar sanarwar, Haidar ya gaji Ahmad Liman, wanda ya yi ritaya a ranar 28 ga Fabrairu, 2025.

 

Haidar, wanda ya kammala karatunsa na kimiyyar siyasa a shekarar 1989 a Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, an nada shi Babban Sakatare a shekarar 2012, kuma ya yi aiki a ma’aikatu da hukumomi gwamnati da dai sauransu.

 

Gwamna Lawal ya bayyana godiya ga shugaban ma’aikata mai barin gado bisa sadaukarwar da ya yi wa jihar.

 

Ya bukaci sabon shugaban ma’aikatan da aka nada da ya kiyaye mutunci tare da bin ka’idojin aikin gwamnati wajen gudanar da ayyukansa.

 

REL/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Dan Asalin Tudun Loess

A watan Janairu na shekarar 1969, Xi Jinping, wanda bai kai shekaru 16 da haihuwa ba a lokacin, ya zo kauyen Liangjiahe da ke arewacin lardin Shaanxi daga birnin Beijing. Ya ce, “Duk inda na je, zan kasance dan asalin tudun Loess.” Shekaru da yawa bayan haka, ya bayyana a cikin wata kasida cewa, “A matsayina na ma’aikacin gwamnati, yankin arewacin Shaanxi shi ne asalina, saboda wurin ne ya dasa mani imanina wanda ba zai canza ba wato yin abubuwa masu alfanu ga mutane a aikace!” (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci