A yi adalci a binciken mutuwar dan kwallon Nijerirya a Uganda —Gwamnatin Sakkwato
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamnatin Sakkwato ta buƙaci a yi adalci a binciken da ake yi kan silar rasuwar ɗan ƙwallon ƙafan nan ɗan asalin jihar, Abubakar Lawal, wanda ya rasu a satin da ya gabata kasar Uganda inda yake taka leda.
Kwamishinan Matasa da Wasanni na jihar, Injiniya Almustafa Muhammad Kofar Marke ne ya sanar da hakan a lokacin da suke karbar gawar margayin a Nijeriya domin jana’izarsa a mahaifarsa sa ke jihar.
Injiniya Kofar Marke ya bayyana baƙin ciki da rashin Abubakar Lawal, wanda ya bayyana a matsayin ɗan kwallon ƙafa na musamman kuma jakada nagari a harkar wasanni.
“Labarin rasuwar nan abar girgiza da taba zuciya ce, domin marigayin ya bayar da gudunmuwa a harkaar ƙwallon ƙafa ta a-zo-a-gani a duniya ta hanyar ƙasashe daban-daban.
“Muna gode wa ofishin jekadancinmu da ya tabbatar da dawowar gawar margayin zuwa gida don yi mata janaza, haka ma makusantan abokansa suma sun yi kokari.”
Injiniya Mustafa ya ƙara tabbatar da goyon bayansu ga iyalan marigayin kamar yadda suka yi tsaye tun sa’adda lamarin ya faru har aka karbi gawar, bisa ga sahalewar gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu.
Dan kwallon Nijeriya Abdullahi Shehu ne ya rako gawar zuwa Nijeriya ya mika ta’aziyarsa ga iyalai da dangin margayin da mutanen Sakkwato da masoya kwallon kafa gaba daya.
“Abubakar Lawal ba kawai abokin hulɗa ba ne, aboki ne a gare ni, yana da karimci da sanin yakamata, ina rokon Allah Ya gafarta masa”.
Margayin ɗan kwallon Nijeriya ne da ya fara buga wasa a Sakkwato da Nasarawa kafin likafa ta ci gaba ya koma kasar Uganda, ya samu nasarori da dama a wasan ƙwallon kafa a lokacin rayuwarsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abubakar Lawal Gawa Ƙwallon ƙafa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara
Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna
Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya
Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.
Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
ShareTweetSendShare MASU ALAKA