Mutanen kasar Amurka sun fito zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da korar Falasdinawa daga Gaza ne, bayan taron da yan jaridu na Trump Da Natanyaho a birnin washintong a jiya Talata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto masu zanga-zangar su na rera taken cewa “gaza ba na sayarwa bane”.

Maganganun Trump a baya-bayan nan, dangane da yankin Gaza dai, ya jawo cece-kuce da dama kan al-amiran a duniya,

A birnin Washington dai mutane sun yi ta kawo batun kare hakkin ‘yan kasa’ da kuma tauya hakkin wata al-umma wacce ta yi shekarun fiye 75 tu na neman hakkinta na komawa kasarta, daga kasashen da suke rayuwa, rayuwa irin ta yan gudun hijira na lokaci mai tsawo.

A lokacin tattaunawar dai shugaba Trump ya janye shawarar maida mutanen gaza daga kasarsu zuwa wata kasa daga cikin kasashen larabawa.

Yace dama su ya bukatar ya kwace iko da Gaza sannan ya dauki matakan kula da shi na wani lokaci, bayan ya cire dukkan boma boman da abubuwan facewa  a yankin sannan ya mikawa HKI yankin.

Har’ila yau shugaban ya kasa samun amincewar majalisar dokokin kasar Amurka dangane da wannan shirin nasa.

Rashida Tlaib da Ilham Umar duk musulmi ne Amurkawa yan majalisar dokokin kasar wadanda suka ki amincewa da ra’ayin na shugabaTrump.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ya fito ƙarara ya goyi bayan shugaban ƙasa wanda ba a cikin jam’iyyarsu yake, Soludo ya ce goyon bayansa ga Tinubu ba sabon abu ba ne.

 

“An samar da waɗannan huluna tun lokacin da Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Anambra kuma kun ga allunan talla da sauran abubuwa da ke bayyana cewa masu ra’ayin kowa ci gaba suna aiki tare ne da juna,” in ji Soludo.

 

“Bayan haka, wannan wata babbar manufa ce da na yi imani da ita sosai, cewa ya kamata dukkan jam’iyyun siyasa da ke ikirarin ra’ayin ci gaba su haɗu a ƙarƙashin wata babbar ƙawance don zurfafa tunani da kawo ci gaba ba kawai a tafarkin dimokuradiyyarmu ba, har ma da ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasarmu.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa kiransa na ganin masu ra’ayin ci gaba sun yi aiki tare ya samo asali ne daga yaƙini da kuma daɗaɗɗiyar alaƙar da ke tsakaninsa da Shugaban Ƙasa.

 

“Idan na ce masu ra’ayin ci gaba su yi aiki tare, kira ne ga duk masu magana kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu… Ina nufin, ba ni da wani uzuri game da hakan.

 

“Shugaba Tinubu abokina ne, abokina ne tun shekaru 22 da suka gabata zuwa yanzu.

 

“Abokina ne, ina goyon bayansa, kuma na gamsu da matakan da ya ɗauka, musamman a fannin tattalin arziki, kuma na bayyana hakan ba sau ɗaya ba, muna kan hanyar ƙwarai kuma muna buƙatar mu ci gaba a haka,” in ji Soludo.

 

Game da halin tsaro a Jihar Anambra, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta ɗauki wani tsari na bai-daya tun daga watan Janairu, biyo bayan zartar da dokar tsaron cikin gida a jihar.

 

“Ana kokarin tunkarar matsalar rashin tsaro ne tun daga tushe. Dukkanin miyagun ‘yan ta’adda sun tsere daga jihar saboda su ne ke yaudarar matasanmu da kuma jefa su cikin aikata laifuka,” in ji shi.

 

Soludo ya ce gwamnati na amfani da matakan karfi da na lallashi don magance matsalar rashin tsaro.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza
  • Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu
  • Hamas ta aike da wasikar yabo ga Yemen kan goyon bayan Gaza
  • Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda
  • Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran
  • PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
  • Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
  • Armenia Ta Tabbatarwa Iran Zata Kula Da Muradunta Bayan Yarjeniya Da Azarbaijan A Amurka