Aminiya:
2025-06-16@00:49:37 GMT

An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka

Published: 5th, February 2025 GMT

A bayan nan ne Amurka ta sanya harajin kashi 25 a kan kayayyakin da ake shigar wa ƙasar daga Canada da Mexico da kuma kashi 10 kan kayayyakin makamashi na Canada, yayin da kayayyakin China za su fuskanci harajin kashi 10.

Sakatariyar yaɗa labaran Fadar White House, Karoline Leavitt, ce ta bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai a ranar Juma’a.

Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri

Ta bayyana cewa “Canada da Mexico suna ba da damar shigar da muguwar ƙwayar nan ta fentanyl da ke kashe Amurkawa da kuma baƙin haure ba bisa ka’ida ba zuwa kasar mu.”

Ta ce Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin wanda zai soma aiki daga ranar Talata, domin magance matsalar shigar da maganin kashe raɗaɗi na fentanyl da matsalar ‘yan gudun hijira da ke shiga Amurka ba bisa ƙa’ida ba.

“Shugaba Donald Trump na ɗaukar ƙwararan matakai don kare Amurkawa daga matsalar maganin na fentanyl. Fentanyl shi ne kan gaba wajen sanadin mutuwar Amurkawa masu shekaru 18 zuwa 45,” in ji Leavitt.

Amurkan dai ta zargi masu safarar miyagun ƙwayoyi na Mexico da kasancewa “kan gaba a duniya wajen safarar” fentanyl da sauran ƙwayoyi, yana zargin akwai ƙawance tsakanin masu safarar da gwamnatin Mexico.

Game da Canada, Fadar White House ta yi ƙarin haske game da ƙaruwar samar da maganin na kashe raɗaɗi na fentanyl da kuma tsallaka wa da shi kan iyaka ba bisa ƙa’ida ba, tana mai cewa: “an kama fentanyl a kan iyakar Arewa a bara wanda zai iya kashe Amurkawa miliyan 9.8.”

An soki China saboda zargin tana taka rawa wajen bayar da tallafi ga kamfanonin sinadarai wajen fitar da fentanyl zuwa ƙasashen waje, inda Fadar White House ta yi iƙirarin cewa: “ba wai kawai China ta gaza wajen daƙile tushen haramtattun ƙwayoyi ba, har ma tana taimaka wa wannan kasuwanci.”

Martanin Canada da Mexico

Ƙasashen Canada da Mexico sun sanar da ɗaukar matakan ramuwar gayya kan harajin da Shugaba Trump ya ɗora wa kayayyakinsu.

A ranar Asabar, Firaminista Justin Trudeau ya ce Canada za ta sanya harajin kashi 25 kan kayayyakin Amurka da suka kai dala biliyan 106.5 a matsayin martani ga harajin Amurka.

Harajin dala biliyan 20 zai fara aiki daga ranar Talata, sannan na dala biliyan 86 zai fara aiki a cikin kwanaki 21, kamar yadda Trudeau ya shaida wa wani taron manema labarai.

Trudeau ya yi gargaɗin cewa harajin zai cutar da Amurka, wacce daɗaɗɗiyar ƙawar ƙasar ta Canada ce.

Ya nemi mutanen Canada su riƙa sayen kayayyakin da aka yi a ƙasar, kuma su riƙa gudanar da hutu a gida maimakon a Amurka.

Ya ce ana kuma duba wasu matakan da ba na haraji ba, da suka haɗa da wasu da suka shafi ma’adanai masu mahimmanci da sayen makamashi da sauran ɓangarorin haɗin gwiwa.

Trudeau ya kuma ƙara da cewa, ƙasashen Canada da Mexico suna aiki tare don fuskantar harajin da Washington ta ɗora wa kayayyakinsu.

Fadar White House ta ce manufar harajin ita ce matsa wa Mexico da Canada da China lamba su ƙara ba da haɗin kai kan daƙile shigar da miyagun ƙwayoyi da tsaron kan iyakoki da hana kwarar baƙin haure shiga ƙasar ta ɓarauniyar hanya.

China ta bi sahu

China a wani mataki na ramuwar gayya ta lafta wa Amurka harajin kaso 15 cikin 100 na kayayakin kwal da na makamashin gas da ake shigar da shi kasar daga Amurka.

Ƙarin harajin a cewar Ma’aikatar Kuɗin Beijing zai fara aiki ne a makon gobe.

A cikin sanarwar da ta fitar ta ɗaukar matakan ramuwa, China ta zargi Amurka a ƙarƙashin Donald Trump da karya ƙa’idojin kasuwanci na ƙasa da ƙasa.

“Gaban kai da Amurka ta yi ita kaɗai ta lafta haraji ya saɓa ƙa’idojin Hukumar Kasuwaci ta Duniya. Wannan ya saɓa wa yarjeniyoyin kasuwanci da tattalin arziƙi tsakanin China da Amurka.”

Bugu da ƙari China ta sanar matakin fara bincike a kan kamfanin fasaha na Google.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fadar White House

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran

Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.

Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

Sai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.

Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.

A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.

Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.

Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.

Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.

A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai