NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana
Published: 5th, February 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da tsawaita wa’adin karɓar kuɗin aikin Hajjin bana.
NAHCON ta ce daga yanzu zuwa 10 ga watan Fabrairu ƙofa a buɗe take ta ci gaba da karɓar kuɗin kujera ga maniyyatan da ke son sauke farali a bana.
Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba An soma rigimar haraji tsakanin China da AmurkaAna iya tuna cewa, da misalin ƙarfe goma sha biyun daren ranar Juma’a 31 ga watan Janairun 2025, ne wa’adin biyan kuɗin kujerun aikin hajjin bana ya cika.
Sai dai cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar NAHCON ta ƙasa, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce tsawaita wa’adin wata dama ce ga maniyyatan da ba su kammala biyan kuɗin kujerar ba.
Hajiya Fatima ta kuma ce NAHCON ta buƙaci shugabannin hukumomin Alhazai na jihohi da su tabbatar sun bayar da haɗin kai na miƙa mata kuɗaɗen alhazan domin tanadar musu masauki a ƙasa mai tsarki.
Tun bayan cikar wa’adin na farko ne NAHCON, ta shaida wa BBC cewa, idan har akwai wani sabon bayani a game da ƙara wa’adin biyan kuɗin to hukumarsu za ta sanar.
NAHCON ta ce daga bayanan da suke samu daga jihohi kawo yanzu mutane sun biya kuɗinsu domin akwai ma waɗanda suka biya kuɗin da ya zarta wanda aka sanar sakamakon hasashen cewa kuɗin kujerar bana zai iya kai wa Naira miliyan 10.
“Yanzu irin waɗannan mutane da suka biya kuɗin da ya zarta na kujerar suna ta murna bayan sanar da kuɗin kujerar ta bana, kuma nan ba da jimawa ba za a mayar musu da sauran kuɗinsu bayan an cire wanda ya kamata,” in ji Hajiya Fatima.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kuɗin Kujera biyan kuɗin
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.
Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDPMai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.
Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.
Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.
Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.
Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.
“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.