HausaTv:
2025-11-03@08:04:20 GMT

Amnesty Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Kama Benjamin Netanyahu

Published: 5th, February 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta kira yi Amurka da ta kama Fira ministan “Isra’ila” Benjamin Netanyahu da yake ziyarar aiki a kasar.

A wasu jerin sakwanni da kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta duniya ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa; Yadda Amurka ta karbi bakuncin Benjamin Netanyahu alhali ana zarginsa da manyan laifuka, yana nuni da cewa ta raina kotun ta kasa da kasa.

Har ila yau kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta kuma kara da cewa; Gwamnatin da ta gabata ta Amurka a karkashin Joe Biden ta yi watsi da duk wani yunkuri na shimfida adalci a duniya, kuma shi ma shugaba Trump abinda yake yi kenan a yanzu.

Wannan ce ziyara ta farko da Fira ministan HKI  Benjamin Netanyahu ya kai zuwa waje, tun bayan da kotun kasa da kasar ta fitar da sammacin kamo shi, saboda aikata manyan laifuka da su ka hada da kisan kiyashi.

A ranar 21 ga watan Nuwamba 2024 ne dai kotun kasa da kasa ta fitar da sammacin a kamo Benjamin Netanyahu da ministansa na yaki Yoav Gallant, saboda laifukan da su ka tafka a Gaza.

A karshe kungiyar kare hakkin bil’adaman ta ce, bai kamata ba  a bai wa masu aikata laifukan yaki akan bil’adama  mafaka.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kare hakkin bil adama Benjamin Netanyahu

এছাড়াও পড়ুন:

Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja

An kama wata matar aure a garin Kuta, hedikwatar Karamar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja, bisa zargin yankar wuyan mijinta, Salisu Suleiman, da wukar girki.

Majiyoyi sun ce matar ta kuma soka wa mijin wuka a idonsa na hagu, lamarin da ya lalata idon gaba ɗaya.

Wata majiya da ta nemi a ɓoye sunanta ta bayyana wa wakilinmu cewa ma’auratan sun samu saɓani ne, inda matar ta jira har sai da mijin ya kwanta barci kafin ta kai masa hari da wuƙa.

Kakakin ’yan sanda na Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ce lamarinya auku ne da safiyar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025.

A cewarsa, “A ranar 1 ga Nuwamba, da misalin ƙarfe 2:30 na asuba, wani Salisu Suleiman na garin Kuta ya samu saɓani da matarsa, Halima Salisu, inda da mijin ya kwanta barci, matar ta ɗauki wuƙa ta yankar masa wuya, sannan ta soka masa a idon hagu.”

SP Abiodun ya ce an garzaya da wanda abin ya faru da shi Asibitin Gabaɗaya na Kuta, daga nan kuma aka mayar da shi Asibitin Ƙwararru na IBB da ke Minna domin ƙarin kulawar likitoci.

Ya ƙara da cewa, “An kama wadda ake zargi, kuma tana tsare a hannun ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da ita a gaban kotu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa