Aminiya:
2025-10-13@15:53:04 GMT

Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye

Published: 13th, October 2025 GMT

Sakamakon farko na zaben shugaban kasar Jamhuriyar Kamaru da ake ci gaba da kirgawa ya nuna jagoran adawa, Issa Tchiroma Bakary, ya samu gagarumin rinjaye a yankunan da a bayan Shugaba Paul Biya ya saba rinjaye.

Shugaba Paul Biya mai shekaru 92 yana fuskantar abokan hamayya 11 cikin har da tsofaffin mukarrabansa, da ma tsoffin ministocinsa da ke neman kujerarsa da ya shafe shekara 43 a kai kuma yake namen wa’adi na takswas.

Cikinsu har da tsohon Ministan Yawon Bude Ido, Bello Bouba Maigari, da tsohon ministan Ayyuka, Bakary, wanda ya yi murabus a watan Yuli domin shiga takara kuma ya sama mafi shahara bayan doka ta haramta wa madugun adawa Maurice Kamto shiga zaben..

Biya ya ki yin tsokaci game da nasarar a lokacin da ya jefa kuri’arsa a birnin Yaounde ranar Lahadi, amma sakamakon farko sun nuna jam’iyyar FSNC wadda Bakary ya tsaya takara ta samu galaba a yankin da a bayan jam’iyyar CPDM ta Shugaba Biya ke da rinjaye.

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno

Wani dan jarida da ke aikin sa ido kan zaben shaida wa wakilimu cewa jam’iyyar FSNC ta samu rinjaye a yawancin runfunan zaben da ke larduna bakwai na birnin Yaounde.

Kowacce daga cikin lardunan na da rumfunan zabe 40 zuwa 50, lamarin da ya mayar da Yaounde fage mai matukar muhimmanci a zaben kasar.

Bakary, wanda dan asalin yankin Garoua ne a yankni Arewa mai Nisa ya kuma doke Bello Maigari a yankin da su biyun suka fito.

Amma duk da haka Jam’iyyar CPDM tana bukatar samun gagarumar goyon bayan a yankin Ambazoniya – Arewa mai nisa da kuma yankin Kudu maso Yamma da kuma Arewa maso Yamma masu amfani da turancin Ingilishi.

Wani dan jarida ya bayyana cewa Bakary ya samu rinjaye a kuri’un da aka jefa a kasashen waje, in banda kasar Rasha.

“Karon farko ke nan tun shekarar 1992 da jam’iyyar adawa ta samu irin wannan rinjaye tun da wuri,” in ji shi.

Wadannan alkaluman wucin gadi ne a yayin da ake jihar Hukuamr Shari’a ta kasar za ta sanar da sakamakon zaben a hukumance cikin makonni biyu da ke tafe.

Ya ci gaba da cewa “Hukumar tana iya sauya sakamakon kuma Kotun Koli tana iya nada duk wanda ta ga ya dace da kujerar.”

Tsarin zaben Kamaru na zagaye daya ne, inda duk wanda ya fi samun kuri’u shi ne ke da nasara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bakary Biya Kamaru Paul Biya

এছাড়াও পড়ুন:

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

A hakila, sha’anin yawon shakatawa na fadada hanyoyin samun kudi ga mutanen Xinjiang.

 

Alkaluman da hukumar kula da harkokin al’adu da yawon shakatawa ta Xinjiang ta samar sun shaida cewa, a yayin hutun bikin murnar kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a kwanakin baya, yankin ya karbi baki masu yawon shakatawa sama da miliyan 18, adadin da ya karu da kashi 11.26% idan aka kwatanta da na bara, kudin da bakin suka kashe ya kai fiye da Yuan biliyan 25, kwatankwacin dalar Amurka sama da biliyan 3.5, wanda kuma ya karu da kashi 11.71%. Hakan ya nuna cewa, aikin yawon shakatawa na Xinjiang yana da makoma mai kyau.

 

A watan Mayu na wannan shekara, an fitar da “Shirin raya sana’o’in al’adu da yawon shakatawa na Xinjiang (2025-2030)”, wanda ya gabatar da makoma mai haske a wadannan fannoni. Wato a cikin shekaru 6 masu zuwa, Xinjiang za ta dukufa a kan raya sana’o’in al’adu da wasanni da yawon shakatawa, wadanda za su shafi kudin Sin da yawansa ya wuce tiriliyan guda, kuma ana sa ran zuwa shekara ta 2030, adadin baki da yankin zai karba zai wuce miliyan 400 a shekara.

 

Bunkasar yawon shakatawa a Xinjiang wani bangare ne na ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na yankin. Hakan ya baiwa mutane kamar Birey damar kyautata zaman rayuwarsu, ya kuma fadada musu hanyoyin samun kudi. Muna da imanin cewa a nan gaba, karin mazauna yankin Xinjiang za su kara samun kudin shiga, tare da kara jin dadin rayuwarsu, kamar yadda malam Aydarbek Birey ya yi. (Mai zane da rubutu: MINA)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa October 12, 2025 Ra'ayi Riga Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka October 7, 2025 Ra'ayi Riga Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang September 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • An Kara Zaburar Da ‘Yan Arewa Game Da Muhimmancin Mallakar Katin Zabe
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya