Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Published: 13th, October 2025 GMT
A hakila, sha’anin yawon shakatawa na fadada hanyoyin samun kudi ga mutanen Xinjiang.
Alkaluman da hukumar kula da harkokin al’adu da yawon shakatawa ta Xinjiang ta samar sun shaida cewa, a yayin hutun bikin murnar kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a kwanakin baya, yankin ya karbi baki masu yawon shakatawa sama da miliyan 18, adadin da ya karu da kashi 11.
A watan Mayu na wannan shekara, an fitar da “Shirin raya sana’o’in al’adu da yawon shakatawa na Xinjiang (2025-2030)”, wanda ya gabatar da makoma mai haske a wadannan fannoni. Wato a cikin shekaru 6 masu zuwa, Xinjiang za ta dukufa a kan raya sana’o’in al’adu da wasanni da yawon shakatawa, wadanda za su shafi kudin Sin da yawansa ya wuce tiriliyan guda, kuma ana sa ran zuwa shekara ta 2030, adadin baki da yankin zai karba zai wuce miliyan 400 a shekara.
Bunkasar yawon shakatawa a Xinjiang wani bangare ne na ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na yankin. Hakan ya baiwa mutane kamar Birey damar kyautata zaman rayuwarsu, ya kuma fadada musu hanyoyin samun kudi. Muna da imanin cewa a nan gaba, karin mazauna yankin Xinjiang za su kara samun kudin shiga, tare da kara jin dadin rayuwarsu, kamar yadda malam Aydarbek Birey ya yi. (Mai zane da rubutu: MINA)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tafi birnin Rome na Ƙasar Italiya, domin halartar taron shugabannin ƙasashe kan sha’anin tsaro.
Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya ce za a fara taron ne a ranar 14 ga watan Oktoba, kuma zai mayar da hankali kan matsalar tsaro da ke addabar yankin Yammacin Afirka.
’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — KwamishinaTaron na ‘Aqaba Process’ an kafa shi ne a shekarar 2015 ta hannun Sarki Abdullah II na Ƙasar Jordan, kuma ana gudanar da shi tare da haɗin gwiwar Jordan da ƙasar Italiya.
Taron na nufin tattauna hanyoyin yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalolin tsaro da ke adabbar ƙasashe daban-daban, musamman a yankin Yammacin Afirka.
Taron zai haɗa shugabannin ƙasashe na Afirka, jami’an leƙen asiri da na tsaro, da wakilan ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na ƙungiyoyin fararen hula, domin tattauna yadda za a magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin.
Za a tattauna kan yadda ƙungiyoyin ta’addanci ke yaɗuwa a Yammacin Afirka, alaƙa tsakanin masu laifi da ’yan ta’adda, da kuma alaƙar da ke tsakanin ta’addanci a yankin Sahel.
Hakazalika, za a tattauna yadda za a daƙile yaɗuwar aƙidar ta’addanci a Intanet da kuma lalata hanyoyin sadarwar da ’yan ta’adda ke amfani da su wajen yaɗa ra’ayoyinsu da ɗaukar sababbin mabiya.
Shugaba Tinubu zai kuma tattauna da wasu shugabannin ƙasashe don neman hanyoyin daƙile matsalar tsaro da ke addabar yankin.
Tinubu ya samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Ambasada Bianca Odumegwu–Ojukwu; Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar.
Sauran sun haɗa daMai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu; Darakta-Janar na Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), Ambasada Mohammed Mohammed; da wasu manyan jami’an gwamnati.